Jump to content

Abd al-Qadir (Sokoto)

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abd al-Qadir (Sokoto)
Rayuwa
Haihuwa 1842
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Mutuwa 1859
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Abd al-Qadir, wanda kuma aka fi sani da Abdulkadir, shi ne Wazirin Sokoto daga shekara ta 1842 zuwa 1859. Ya gaji mahaifinsa, Gidado dan Laima (1817–1842), kuma daga bisani aka gaje shi da Ibrahim Khalilu (1859–kimanin 1874).

Kafin nada shi a matsayin waziri, Abdulkadir ya halarci farmaki 25 a ƙarƙashin Sarkin Musulmi Muhammed Bello[1], da kuma farmaki 4 tare da kawunsa Abu Bakr Atiku.

Ya kasance ɗaya daga cikin amintattun Sarkin Ali Babba bin Bello kuma ɗan Nana Asma'u ne.[2]

Zamansa a matsayin Wazirin Sokoto ya kasance mai tasiri, duk da cewa akwai wasu iyakoki a ƙarfin ikonsa. Abdulkadir yana da hannu wajen korar Umaru Nagwamatse daga mulkin Katuru. Umaru yana da suna a matsayin ɗan sarki mai ƙarfi, mai cin gashin kansa kuma mai nasara, amma daga baya an tabbatar da cewa bai dace da shugabanci ba.

Daga baya Umaru ya koma ƙasar kudu inda ya kafa daular Fulani a Kontagora.[3]

Duk da wannan tasiri, akwai wasu iyakoki a kan ikon Abdulkadir. Lokacin da Bukhari, Sarkin Hadejia, ya karɓi mulki ta hanyar amfani da ƙarfi, an ɗora wa Abdulkadir alhakin shawo kan lamarin. Ya nufi Katagum inda ya kira Bukhari, amma Bukhari ya yi barazana da dakarunsa.

Daga nan aka ayyana Bukhari a matsayin ɓarawo ko mai tawaye, kuma aka naɗa Ahmad, ɗan’uwan Abdulkadir, a matsayin sarki.

Bukhari ya nemi taimako daga daular Borno. An tura yakoki guda biyu: ɗaya ƙarƙashin jagorancin Ahmad, ɗaya kuma na Abdulkadir, amma duk sun kasa cimma nasara.

A ƙarshe, Bukhari ya kashe ɗan’uwansa Ahmad kuma ya ci gaba da mulkin Hadejia da kansa.

  1. Last, M. D. The Sokoto Caliphate. Humanities Press. shafi na 156
  2. Beverley Mack, Jean Boyd. Educating Muslim Women: The West African Legacy of Nana Asma'u 1793–1864. Kube Publishing, 2013. shafi na 118
  3. Last. The Sokoto Caliphate, shafi na 159