Jump to content

Acacia Bandubola Mbongo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Acacia Bandubola Mbongo
Minister of Economy (en) Fassara

26 ga Augusta, 2019 - 26 ga Afirilu, 2021 - Jean-Marie Kalumba Yuma (mul) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Kisangani
ƙasa Jamhuriyar dimokuradiyya Kwango
Karatu
Makaranta Université protestante au Congo (mul) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa, ɗan kasuwa da civil servant (en) Fassara

Acacia Bandubola Mbongo, (née Acacia Bandubola ), 'yar kasuwa ce kuma 'yar siyasa ta ƙasar Congo, wacce ta yi aiki a matsayin Ministar Tattalin Arziki ta Ƙasa a Majalisar Zartaswar Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo, daga ranar 26 ga watan Agusta 2019, har zuwa watan Maris 2023. [1]

Tarihi da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Bandubola a birnin Kisangani, ɗiya ga Henriette Mbokoso Bokwetenge da Raphael Bandubola. Ta halarci CS Okapi, makaranta mai zaman kanta a Kisangani, inda iyayenta ke zaune a lokacin. A cikin shekarar 1994, Acacia Bandubola ta ƙaura zuwa Kinshasa, babban birni kuma birni mafi girma a ƙasar. Ta ci gaba da karatu a Lycée Bosangani daga shekarun 1994 zuwa 1999. A cikin shekarar 2000, ta kammala karatu tare da Diploma na Makarantar Jiha daga Lycée Molière. Ta yi digirin digirgir a fannin kasuwanci daga Jami'ar Furotesta da ke Kongo. [2]

A cikin kasuwanci

[gyara sashe | gyara masomin]

Bandubola ta yi aiki a Ecobank, FINCA, Banque Internationale pour l'Afrique au Congo (BIAC), da Vodacom. Ta kuma yi aiki a wani kamfani mai ba da shawara kan tattalin arziki a Faransa. [2]

Bandubola ta fara fafutukar ta na siyasa tun tana ɗaliba, domin adawa da manufofin zalunci na Mobutu Sese Seko. Ta kasance tana goyon bayan jam'iyyun siyasa da dama yayin da take cikin Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo, ciki har da Envol da RNS. [2]

Yayin da take aiki a Faransa, an gabatar da ita ga akidar Étienne Tshisekedi kuma ta shiga jam'iyyar siyasa ta Union for Democracy and Social Progress (UDPS). Ta zama mai goyon bayan UDPS a yawancin kafofin watsa labarai (radio da talabijin) a Yamma. A cikin majalisar ministocin da aka sanar a ranar 29 ga watan Agusta, 2019, an naɗa ta a matsayin ministar tattalin arzikin ƙasa, inda ta maye gurbin Joseph Kapika, wanda ya riƙe muƙamin daga watan Afrilu 2017, har zuwa watan Agusta 2019. [1] [2]

A matsayinta na minista, ta yi Allah-wadai da yadda wasu ‘yan kasuwa ke yi a DRC, suna ƙara farashin kayayyakin masarufi, da suka haɗa da garin masara, da sukari da shinkafa, saboda fargabar Coronavirus. Ta ba da shawarar cewa gwamnati, 'yan kasuwa da jama'a su yi aiki tare don tabbatar da daidaiton farashi yayin bala'in. A takaice dai, ta ba da shawarar cewa ya kamata gwamnati ta daidaita farashin kayayyaki, lokacin da 'yan kasuwa ke yin hauhawar farashin kayayyaki. [3]

Acacia Bandubola Mbongo uwa ce mai aure. [2]

  1. 1.0 1.1 Government of DR Congo (5 September 2019). "Announcement of The New Government of the Democratic Republic of the Congo" (Translated from the original French Language). Embassy of DR Congo to the United States. Retrieved 21 March 2020. Cite error: Invalid <ref> tag; name "1R" defined multiple times with different content
  2. 2.0 2.1 2.2 2.3 2.4 7sur7.cd (6 September 2019). "DRC: Here is the portrait of the new Minister of the Economy Acacia Bandubola Mbongo" (Translated from the original French Language). Kinshasa: 7sur7.cd. Retrieved 21 March 2020. Cite error: Invalid <ref> tag; name "2R" defined multiple times with different content
  3. Actualite.cd (20 March 2020). "Acacia Bandubola writes to Jacques Kyabula: "In the event of a breakdown in the market balance which leads to an excessive rise in prices, the government fixes prices"" (Translated from the original French Language). Kinshasa: Actualite.cd. Retrieved 21 March 2020.