Jump to content

Adele Ajosun

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Adele Ajosun
Oba na Lagos

Rayuwa
Haihuwa Lagos,, 
Mutuwa Lagos,, 1837
Makwanci Masarautar Benin
Ƴan uwa
Mahaifi Ologun Kutere
Sana'a
Sana'a ɗan kasuwa da slave trader (en) Fassara

Oba Adele ko Adele Ajosun (ya rasu a shekarar 1837) ya yi sarauta sau biyu a matsayin Oba na Legas; na farko, daga shekarun c1811 zuwa 1821, da kuma karo na biyu daga shekarun 1835 zuwa 1837. Mahaifinsa shi ne Oba Ologun Kutere da ’yan uwansa su ne Obas Osinlokun da Akitoye, don haka layin Ologun Kutere ya kasance kan gaba a cikin Obaship na Legas.[1]

Adele ya hau Obaship na Legas bayan kimanin shekara 5 da rasuwar mahaifinsa Ologun Kutere. Wasu majiyoyin rubuce-rubuce da na baka sun lura cewa Ologun Kutere ya so Adele ya zama Oba saboda amincin Adele ga Ologun Kutere. Masanin tarihi John. B. Losi ya rubuta game da kulawar Adele game da kadarorin Ologun Kutere yayin da ’yan’uwan Lander (Richard da John Lander) suka lura da ƙwarewar injin Adele.[2]

A zamanin Adele addinin Musulunci ya yaɗu a Legas kuma an ce farin jininsa ya ragu a tsakanin 'yan Legas saboda 'ya'yansa sun gabatar da mashin din Egun, wanda a lokacin ake ganin bai dace ba.[3]

Juyin mulkin Osinlokun da kuma gudun hijirar Adele zuwa Badagry

[gyara sashe | gyara masomin]

A tsakanin shekara ta 1820 ko 1821, kamar yadda al’adar ta kasance kafin shekara ya 1852 lokacin da Legas ta ƙara samun ‘yancin kai daga Daular Benin, Adele ya yi yunkurin raka gawar Ologun Kutere zuwa Benin don binne shi, amma Osinlokun da magoya bayansa sun hana Adele yin hakan da karfi, kuma a cikin haka ne suka kwace Obaship daga Adele. Yanzu dai an kai Adele gudun hijira zuwa Badagry inda ya zama shugaban garin. A cikin shekarar 1825, yayin da yake Badagry, Adele ya yi ƙoƙari ya karɓe sarautar Legas da ƙarfi tare da taimakon sojojin ruwa na Burtaniya amma ƙoƙarinsa ya ci tura.[4] An ba da rahoton cewa ya nutse cikin ɓacin rai lokacin da fashewar foda ta lalata masa gida, kadarori, da mabiyansa.

Wa'adi na biyu bayan Idewu Ojulari ya kashe kansa

[gyara sashe | gyara masomin]

Osinlokun ya rasu a shekarar 1829 kuma ɗansa Idewu Ojulari ya gaje shi.

Bayan da Oba Idewu Ojulari ya tilasta wa Oba na Benin (wajen shekarun 1834/5) ya kashe kansa, ya kamata a naɗa kanin Idewu yarima Kosoko a matsayin sarki amma saboda halin da Kosoko yake da shi wanda ya sa ya ɗauki wata mace da aka aura da Eletu Odibo, rikicin da ya biyo baya ya hana Eletu Odibo ɗora Kosoko. Sakamakon haka, an gayyaci Adele (kawun Kosoko da Idewu) daga Badagry ya zama Oba.[2][3]

Aurensa da Madam Tinubu

[gyara sashe | gyara masomin]

Yayin da ya ziyarci Abeokuta a matsayin Oba da aka yi gudun hijira a shekarar 1833, Madam Tinubu ta burge Adele kuma ya aure ta. Sun koma Badagry wanda bisa ga al'ada ya kasance wurin mafaka ga sarakunan Legas kuma shine inda Tinubu ya yi amfani da haɗin gwiwar Adele don gina babbar kasuwancin taba, gishiri, da bayi. [5]

Adele ya rasu a shekara ta 1837 kuma ɗansa Oluwole ya gaje shi a matsayin Oba.[6]

Adele ya samu damar kasancewa Obaship na Legas bayan kimanin shekara 5 da rasuwa mahaifinsa Ologun Kutere. Wasu majiyoyin rubutu da na baka sun lura cewa Ologun Kutere ya buƙaci Adele ya zama Oba saboda aminci na Adele ga Ologun Kutere. Masanin tarihi John. B. Losi yayi rubutu game da kulawar Adele gameda da kadarorin Ologun Kutere yayin da ’yan’uwan Lander ( Richard da John Lander ) suka lura da ƙwarewar injin Adele.

A zamanin Adele, addinin Musulunci ya yaɗu a Legas kuma farin jinin sa ya ragu a tsakanin 'yan Legas saboda 'ya'yansa sun gabatar da mashin din Egun, wanda a lokacin ake ganin bai dace da al'adar su ba.

  1. Mann, Kristin (13 April 2024). Slavery and the Birth of an African City: Lagos, 1760-1900. Indiana University Press, 2007. p. 45. ISBN 9780253348845.
  2. 1 2 Mann, Kristin (13 April 2024). Slavery and the Birth of an African City: Lagos, 1760-1900. Indiana University Press, 2007. pp. 46–49. ISBN 9780253348845.
  3. 1 2 Smith, Robert (January 1979). The Lagos Consulate, 1851-1861. University of California Press, 1979. pp. 14–17. ISBN 9780520037465.
  4. A. Orugbani (13 April 2024). Nigeria since the 19th century. Paragraphics, 2005. p. 74. ISBN 9789782954381.
  5. Qeturah (20 March 2016). "Madam Tinubu". Guardian Life. Archived from the original on 24 December 2016. Retrieved 23 December 2016.
  6. A. Orugbani (13 April 2024). Nigeria since the 19th century. Paragraphics, 2005. p. 74. ISBN 9789782954381.