Ahmed Hassan Barata

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ahmed Hassan Barata
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

6 ga Yuni, 2011 - 6 ga Yuni, 2015 - Ahmad Abubakar
District: Adamawa South
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

29 Mayu 1999 - ga Yuni, 2003
District: Guyuk/Shelleng
Rayuwa
ƙasa Najeriya
Karatu
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Ahmed Hassan Barata ya kasance dan siyasar Najeriya da aka zaba a matsayin dan Majalisar dattijai, mai wakiltar Adamawa ta Kudu a Adamawa,Najeriya a zaben watan Aprilu ta shekara, 2011. Ya tsaya takara a karkashin inuwan jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP).

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

An zabi Barata a matsayin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Guyuk/Shelleng a watan Mayu ta shekarar,1999; mukamin da ya rike har zuwa watan Mayu, 2003.[1]a kara tsayawa takara karo na biyu a mazabar shi, amma ya sha kayi a hannun James Audu Kwawo na Jam'iyyar Action Congress.[1]

Barata yaci zaben fidda gwani na jam'iyyar (PDP) a shekarar 2011 na shiyar Adamawa ta Kudu.Ta samu kuri'u 738, a inda ya kada sanata mai ci Grace Folasade Bent wanda yasamu kuri'u 406.[2] Bent, wacce ake tsammanin tasamu fifiko daga shugabannin jam'iyyar (PDP), daga bisani tayi da'awar samun nasaran lashe zaben na fidda gwani.[1]. Duk da cewa ana akan duba da'awarta, wani Alkali ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ta canza sunan Barata daga jerin sunayen yan takara da na Bent.[3] Daga bisani hukumar zabe ta (INEC) tayi watsi da da'awar Bent, da kotun daukaka kara dake Abuja, da kuma mashawartan jam'iyyar (PDP).[1]

A zaben watan Aprilu na shekarar 2011, Barata ya lashe zaben da kuri'u 101,760, akan abokin takaransa Mohammed Koiraga Jada na Jam'iyyar Action Congress of Nigeria mai kuri'u 66,525.[4]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 1.2 1.3 https://peoplepill.com/people/ahmed-hassan-barata
  2. Joe Nwankwo (7 March 2011). "Adamawa South - Opponent Wants Court to Delist Folasade Bent". Daily Independent. Retrieved 2011-05-06.
  3. Emmanuel Ogala (February 16, 2011). "Court orders electoral body to endorse three senators". Next. Retrieved 2011-05-06.[permanent dead link]
  4. "Collated Senate results". INEC. Archived from the original on 2011-04-19. Retrieved 2011-05-06.