Dutsen ZumaDutsen Zuma babban dutse ne wanda yake a Jihar Neja a kusa da babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja. Dutsen yana kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna daga unguwar Madalla, kuma a wasu lokutan ana kiranta da "Kofar Abuja daga Suleja". Dutsen Zuma yana da tsawo kusan. 300 metres (980 ft) sama da kewayensa.
Yau 25 ga watan Ogusta na 2023
Ga wasu muhimman abubuwa na tarihi da suka faru a wannan rana.
1920: Mata a Amurka suka sami 'yancin jefa ƙuri'a, lokacin da aka tabbatar da gyare-gyare na 19 ga Kundin Tsarin Mulki na Amurka.
1914: Daular Usmaniyya ta shiga yakin duniya na daya ne ta hanyar kulla kawancen sirri da kasar Jamus. Wannan shi ne mafarin shigar daular Usmaniyya a cikin rikicin.
2011: Ƴan tawayen Libya suka ƙwace birnin Tripoli, lamarin da ya zama wani gagarumin sauyi a yaƙin basasar Libya da kuma hamɓarar da gwamnatin Muammar Gaddafi.
1970: Cadi ta ayyana ƴancin kai daga ƙasar Faransa inda ta zama Jamhuriyar Chadi
Ƙasar Denmark na shirin haramta gangamin kona Kur'ani da sauran litattafan addini masu tsarki saboda dalilan tsaro da kuma huldar diflomasiyya.
Kasashen Mali, Burkina Faso da Gine sun lashi takobin shigarwa Nijar fada da Ecowas tun bayan barazanar da ƙungiyar tayi na yaƙar gwamnatin soji ta Jamhuriyar Nijar idan ta cika wa'adin kwana bakwai da ta bata ba tare da miƙa mulki ga fararen hula ba.
Shugabannin Jamhuriyar Jama'ar Kasar Sin sun gabatar da taswirar abubuwan dake kan gaba wajen raya tattalin arzikin kasar Sin a watanni 6 na karshen bana.
Jami'an 'yan sandan jihar Anambra sun tabbatar da mutuwar ma'aurata, da ƴaƴansu biyu da ƙarin wasu mutanen biyu a yankin Nkwele Ezunaka da ke garin Onitsha.