Bashir Zubairu
| Rayuwa | |
|---|---|
| Haihuwa | 28 Mayu 1968 (57 shekaru) |
| ƙasa | Najeriya |
| Sana'a | |
| Sana'a |
ɗan siyasa da legislator (en) |
Bashir Zubairu ɗan siyasar Najeriya ne a matakin majalisar wakilai.[1] A yanzu haka ya zama ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Birnin-Gwari/Giwa a majalisar wakilai ta ƙasa ta 10.[2] Ya ɗauki nauyin kudirori 7 tare da gabatar da kudurori da dama a majalisar dokokin ƙasar.
Aikin siyasa
[gyara sashe | gyara masomin]Honorabul Bashir Zubairu ɗan siyasan Najeriya ne a yanzu haka yana wakiltar tarayya mai wakiltar mazaɓar Birnin Gwari/Giwa a jihar Kaduna. Ya shiga siyasa ya kuma lashe zaɓen mazaɓar sa na majalisar wakilai da kuri’u 41,023. An zaɓe shi a matsayin ɗan majalisar wakilai ta 10 a shekarar 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC).[3]
Zubairu ya riƙe muƙamin kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna a zamanin gwamnatin Gwamna Ahmad Muhammad Makarfi, kafin ya zama majalisar. Matsayin da ya taka a majalisar dokokin jihar ya haɗa da sa ido kan ayyukan majalisa da bayar da gudummawa ga tsara manufofi a matakin jiha.
Baya ga harkar siyasa, Zubairu yana riƙe da sarautar gargajiya ta Ciroman Birnin Gwari, matsayin da ke nuna jagoranci da karɓuwar al’adu a cikin garin Kaduna.
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "10th National Assembly Members". orderpaper.ng. Retrieved 2024-11-25.
- ↑ Ogbeni, Go (2024-06-20). "Honorable members full profile: HON. ZUBAIRU BASHIR USMAN". The Green Chamber. Archived from the original on 2024-12-29. Retrieved 2024-11-25.
- ↑ Ogboni, Conf (2024-11-14). "Farmers lost over N100m in Kaduna maize farm attacks — Zubairu". Daily Trust. Retrieved 2024-11-25.