Jump to content

Batilda Salha Burian

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Batilda Salha Burian
Member of the National Assembly of Tanzania (en) Fassara

2005 - 2010
Rayuwa
Haihuwa 19 Oktoba 1965 (59 shekaru)
ƙasa Tanzaniya
Harshen uwa Harshen Swahili
Karatu
Makaranta University of London (en) Fassara
Harsuna Turanci
Harshen Swahili
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Batilda Salha Burian (an haife a ranar 19 ga watan Oktoba, 1965) 'yar siyasar ƙasar Tanzaniya ce kuma jakadiya.[1] Ita a halin yanzu; kwamishiniyar Yanki ce ta yankin Tanga.[1]

Tarihin Rayuwa

[gyara sashe | gyara masomin]

Burian ta sami digiri na uku a Kwalejin Jami'ar London a shekarar 1992. [2]

Ta yi wa'adi biyu a majalisar, daga shekarun 2000 zuwa 2005 sannan a shekarun 2006 zuwa 2010.[3] Tsakanin wa'adinta a majalisar, ta kasance mataimakiyar ministar ci gaban al'umma, jinsi da yara. Bayan Majalisar, ta zama Babbar Kwamishiniya (ko Jakadiyar Tanzaniya a Kenya).[4] A lokacin da take riƙe da muƙamin jakadiyar ƙasar Kenya, ta ci gaba da karfafa hulɗar dake tsakanin ƙasashen biyu, inda ta bayyana cewa, ƙasashen biyu suna da ma'ana sosai a fannin al'adu da muhalli.[5] A cikin shekarar 2015, ta zama jakadiyar Tanzaniya a Japan.[5]

Burian ta jagoranci taron sauyin yanayi na duniya III a shekarar 2009 a Geneva kuma ita ce wakiliyar dindindin na Tanzaniya a Hukumar Kula da Muhalli ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNEP).[5]

  1. 1.0 1.1 Mwangonde, Henry (6 February 2015). "Burian Moved to Japan from Kenya as Ambassador". The Citizen. Archived from the original on 13 July 2019. Retrieved 19 July 2015.
  2. "Hon. Dr. Batilda Salha Burian". Parliamentary Online Information System. The Parliament of Tanzania. Retrieved 19 July 2015.
  3. "Message from the High Commissioner Dr. Batilda Salha Burian". Tanzania: High Commission, Nairobi. Archived from the original on 20 July 2015. Retrieved 19 July 2015.
  4. "Message from the High Commissioner Dr. Batilda Salha Burian". Tanzania: High Commission, Nairobi. Archived from the original on 20 July 2015. Retrieved 19 July 2015.
  5. 5.0 5.1 5.2 "Diplomacy of Development: 'Tanzania - Kenya Ties Built to Last'". Diplomat East Africa. 6 May 2014. Archived from the original on 21 July 2015. Retrieved 19 July 2015.