Jump to content

Chris Ngoro Agibe

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Chris Ngoro Agibe
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya,

11 ga Yuni, 2019 -
Rayuwa
Haihuwa 1961 (64/65 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Christopher Ngoro Agibe ɗan siyasan Najeriya ne kuma injiniya. Ya kasance memba mai wakiltar mazabar tarayya ta Boki/Ikom a majalisar wakilai.[1][2]

Rayuwar farko, ilimi da aikin siyasa

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Chris Ngoro Agibe a shekarar 1961 kuma dan jihar Cross River ne. Ya kammala karatunsa na sakandare a Comprehensive Secondary School Ikom, Jihar Kuros Riba a shekarar 1978. Ya yi digirinsa na farko a fannin Injiniya a Jami’ar Ife, Ile-Ife, Jihar Osun a shekarar 1984. An zabe shi a matsayin dan majalisar tarayya a 2019 kuma ya yi aiki har zuwa 2023. Bisong Victor Abang ya gaje shi. Tsakanin 1986 zuwa 1990, ya yi aiki a matsayin Jami'in Hukumar, NA-Army Engineering. Ya kasance Shugaban Makamashi Mai Dorewa, Kamfanin Simintin United daga 2007 zuwa 2012.[3]

  1. Legislator Details - ConsTrack Track and Report on Governement Funded Projects in Nigeria". www.constrack.ng. Retrieved 2025-01-02.
  2. Citizen Science Nigeria". citizensciencenigeria.org. Retrieved 2025-01-02
  3. "Hon. Agibe Ngoro biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2025-01-02