Jump to content

Dennis Nnamdi Agbo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Dennis Nnamdi Agbo
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya,

Rayuwa
Haihuwa 15 ga Maris, 1964 (61 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Dennis Nnamdi Agbo (an haife shi ranar 15 ga watan Maris 1964) ɗan siyasan Najeriya ne. A yanzu haka ya zama ɗan majalisar wakilan Najeriya mai wakiltar mazaɓar Igbo-Eze ta Arewa/Udenu na jihar Enugu a majalisar wakilai ta ƙasa ta 10. [1] [2]

A shekarar 2024, Dennis Nnamdi Agbo na jam’iyyar Labour Party (LP) ya samu nasarar lashe kujerar ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Igbo-eze North/Udenu bayan da kotun sauraron ƙararrakin zaɓe ta soke nasarar da Simon Atigwe ya samu. Atigwe na jam’iyyar PDP ne ya lashe zaɓen da aka yi a watan Fabrairun 2024, amma Agbo ya ƙalubalanci sakamakon. [3] [4]

A ranar 14 ga watan Agusta ne kotun ta yanke hukunci kan goyon bayan Agbo, inda ta soke kuri’u 2,000 na Atigwe tare da tabbatar da Agbo a matsayin wanda ya yi nasara na gaskiya bisa sakamakon zaɓen shekarar 2023. [5] [6]

  1. Odunewu, Olusegun (2024-10-09). "Appeal Court reinstates LP's Dennis Agbo, sacks PDP's Simon Atigwe in Enugu". National Daily Newspaper (in Turanci). Archived from the original on 2025-06-01. Retrieved 2024-12-24.
  2. "Dennis Agbo: l'm Fulfilled Giving my People Quality Representation – THISDAYLIVE". www.thisdaylive.com. Retrieved 2024-12-24.
  3. Bankole, Idowu (2024-10-09). "Appeal Court sacks Enugu PDP Rep, returns Agbo of Labour Party". Vanguard News (in Turanci). Retrieved 2024-12-24.
  4. Ugwu, Francis (2024-08-14). "Tribunal sacks Enugu Rep member, declares LP candidate winner". Daily Post Nigeria (in Turanci). Retrieved 2024-12-24.
  5. sunnews (2024-08-16). "Labour Party reclaims National Assembly seat". The Sun Nigeria (in Turanci). Retrieved 2024-12-24.
  6. Ede, Raphael (2024-02-04). "Enugu rerun: PDP wins federal constituency seat". Punch Newspapers (in Turanci). Retrieved 2024-12-24.