Walter Miller
| Rayuwa | |
|---|---|
| Haihuwa |
Honiton (en) |
| ƙasa | Birtaniya |
| Mutuwa | Jos, 27 ga Augusta, 1952 |
| Makwanci | Jos |
| Sana'a | |
| Sana'a | Mishan da mai aikin fassara |

Dr. Walter Richard Samuel Miller Wanda aka fi sani Dr.Miller(an haife shi a 1872 – ya rasu 27 ga Agusta, 1952) ya kasance mishanin Kirista daga Church Missionary Society wanda ya shahara a Najeriya, musamman Arewacin ƙasar. Shi ne wanda ya kafa al’ummar mishan ta Wusasa dake Zaria, kuma ya taka muhimmiyar rawa wajen fassara Littafin Baibûl zuwa harshen Hausa.
Rayuwa ta farko
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Dr. Miller a shekara ta 1872 a Burtaniya. Ya karanci ilimin likitanci da na addini kafin ya tafi aikin mishan a Afirka.[2]
Zuwa Najeriya da Aikin Mishan
[gyara sashe | gyara masomin]A cikin shekarar 1900, Dr. Miller ya zo Najeriya tare da tawagar Bishop Tugwell domin yada bishara a Arewacin Najeriya. Bayan ƙalubale da suka fuskanta a Kano, a shekarar 1902 sun sami izinin Sarkin Zazzau, Aliyu Kwasau, Miller da abokinsa Bargery su kafa sansani a Zaria. Daga nan ne Dr. Miller ya kafa sansanin Wusasa, wanda ya zama cibiyar mishan da makarantu da asibitoci.[3]
Fassarar littafin Bible
[gyara sashe | gyara masomin]Dr. Miller ya jagoranci aikin fassarar Littafin Bible zuwa harshen Hausa tare da taimakon J.T. Umar da P.A. Yusuf. Wannan fassarar an kammala ta a shekara ta 1931 kuma aka wallafa ta a shekara ta 1932 wannan fassara ta taimaka wajen yada Addinin Kiristanci a tsakanin Hausawa.
Haduwa da Isawa
[gyara sashe | gyara masomin]Ya yi hulɗa da ƙungiyar (Isawa) wata ƙungiyar Musulmai inda suka yarda ya koyar da su daga Littafin Bible bayan rasuwar jagoransu Malam Yahaya a 1913.
Mutuwa
[gyara sashe | gyara masomin]Dr. Miller ya rasu a shekarar 1952, kuma an binne shi a St. Bartholomew’s Church da ke Wusasa. Har yanzu Wusasa tana daga cikin wuraren da ke nuna haɗin kai tsakanin Musulmai da Kiristoci a Najeriya.