Emmanuel Ukpong-Udo
11 ga Yuni, 2019 - ← Iboro Ekanem District: Ikono/Ini | |||
| Rayuwa | |||
| Haihuwa | 2 Disamba 1975 (50 shekaru) | ||
| ƙasa | Najeriya | ||
| Sana'a | |||
| Sana'a | ɗan siyasa | ||
Emmanuel Ukpong-Udo (an haife shi a ranar 2 ga watan Disamba, 1975) [1] ɗan siyasa ne a Najeriya, mai taimakon jama'a kuma wakili na gaskiya a Majalisar Wakilai ta Tarayya a Najeriya. [2] Ya wakilci mazaɓar tarayya ta Ikono / Ini a Majalisar Dokokin Najeriya.[2] Ya kasance Babban tsohon Mataimaki na Musamman (SSA) ga Ministan harkokin kasa, Gidaje da Ci gaban Birane a Najeriya (2014-Mayu 2015), [1] kuma shine jagoran Siyasa na yanzu a ƙaramar hukumar Ikono dake Jihar Akwa Ibom, Najeriya.[1]
Emmanuel Ukpong-Udo yana da farin jini a wajen mutanen mazaɓarsa saboda shirye-shiryen ci gaba da tallafi da yake yi.[3] Ayyukansa na kyautatawa sanannu ne a tsakanin mutanen mazaɓar tarayya ta Ikono / Ini, abokan siyasa [3] da kungiyoyi a Najeriya. A bikin bayar da lambar yabo karo na shida na Leadership Excellence (LEEX), wanda Igbere TV ta shirya, an ba shi kyauta ta Mafi Kyawun Ɗan Majalisar wakilai a fannin Karfafa jama'a.[4]
Bayan siyasa da taimakon jama'a, Emmanuel Ukpong-Udo kwararre ne a fannin tsaro da lafiyar ma'aikata.
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ 1.0 1.1 1.2 "National Assembly | Federal Republic of Nigeria". nass.gov.ng. Retrieved 2024-11-05.
- ↑ 2.0 2.1 Utip, Udeme (2023-05-06). "Akwa Ibom: INEC declares YPP candidate winner of Reps seat". Tribune Online (in Turanci). Retrieved 2024-11-05.
- ↑ Kalu, Nicholas (November 2, 2024). "A'Ibom lawmaker gets award for leadership, humanity ". The Nation.