Esther Soyannwo
| Rayuwa | |
|---|---|
| Sana'a |
Esther Oladunni Soyannwo (née Ososami) malamar Najeriya ce kuma yar siyasa. A shekara ta 1964 ita ce mace ta farko da aka zaba a majalisar wakilai, amma ta kasa samun kujerar ta.[1]
Tarihin Rayuwa
[gyara sashe | gyara masomin]Soyannwo ta yi karatu a makarantar ‘yan mata ta CMS da ke Legas kuma ta yi aiki a matsayin malami. Mahaifiyar 'ya'ya shida, ta shiga siyasa a shekarun 1950, ta shiga kungiyar Action Group kuma ta zama mai fafutuka a bangaren mata a shekarar 1953. An zabe ta a karamar hukumar Ijebu ta Kudu,[2] kuma daga baya ta zama 'yar takara daya tilo a kungiyar Action Group a zaben 'yan majalisa na 1964.[3] Dan uwanta, wani hamshakin dan kasuwa a Ijebu ne ya dauki nauyin yakin neman zabenta, ya ba ta fam 2,000. Kungiyar mata ta Ijebu kuma ta taimaka mata yakin neman zabe. Ta doke abokin hamayyarta na jam'iyyar National Democratic Party ta Najeriya Sanya Onabamiro da kuri'u 18,232 zuwa 2,149, daya daga cikin sabbin 'yan takarar kungiyar Action da suka yi nasara a yankin yammacin kasar. Sai dai zaben nata ya haifar da tashin hankali kuma jam’iyyar ta ba ta shawarar cewa zai yi matukar hadari idan ta hau kujerar ta.[4]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ STRIFE IN NIGERIA: PARTY HITS BACK; Loser in Vote See Threat to Political Existence The New York Times, 14 November 1965
- ↑ Nigerian Women Mobilized", Institute of International Studies, 1982, p263
- ↑ Flora Nwapa (1987) Women in Politics
- ↑ Catherine Coquery-Vidrovitch (2018) African Women: A Modern History p185