Gilbert Nnaji

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Gilbert Nnaji
Ɗan Adam
Bayanai
Jinsi namiji
Bangare na Majalisar Wakilai (Najeriya)
Ƙasar asali Najeriya
Suna Gilbert
Shekarun haihuwa 18 ga Yuli, 1966
Sana'a ɗan siyasa
Muƙamin da ya riƙe mamba a majalisar dattijai ta Najeriya, mamba a majalisar dattijai ta Najeriya, mamba a majalisar wakilai ta Najeriya, shugaba da mamba a majalisar wakilai ta Najeriya
Ɗan bangaren siyasa People's Democracy Party (en) Fassara

Gilbert Emeka Nnaji (an haife shi ranar 18 ga watan Yulin 1966 a Umunike, Enugu ta Gabas, Nigeria) ɗan siyasar Najeriya ne.[1] Shine ɗan majalisar dattawa mai wakiltar yankin Enugu ta gabas a majalisar dattawan Najeriya.[2] Ya kasance Sanata a Majalisar Dattawan Najeriya ta 8.

Ya yi karatun firamare a Community Primary School, Amoji, Nike. Daga nan ya wuce makarantar Boys High School Awkunanaw inda ya yi karatunsa na Sakandare. Daga nan ya halarci Jami’ar Najeriya da ke Nsukka inda ya kammala karatunsa na B.Sc a fannin Banki da Kuɗi.

Gilbert Nnaji ya fara harkar siyasa ne a lokacin da ya zama shugaban ƙaramar hukumar Enugu ta Gabas daga shekarar 1997 zuwa 1998. An sake zaɓen shi a matsayin shugaban ƙasa daga shekarar 1999 zuwa 2002.

Gilbert ya tsaya takarar majalisar wakilai ta tarayya kuma ya yi nasara a shekara ta 2003. Ya kasance a majalisar wakilai ta tarayya har sau biyu. Ya kamata a lura da cewa shi ne mataimakin shugaban majalisar wakilai a lokacin da yake majalisar wakilai ta tarayya.[3][4]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://saharareporters.com/2019/04/06/court-dismisses-suit-against-nnamanis-election
  2. https://leadership.ng/
  3. https://www.thisdaylive.com/index.php/2019/04/09/communication-minister-faults-senate-committee-on-104-abandoned-projects/
  4. https://thenationonlineng.net/enugu-east-nnaji-loses-senatorial-seat-to-nnamani/

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]