Jump to content

Gladys Adda

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Gladys Adda
Rayuwa
Cikakken suna Gladys Scialom da جلاديس شالوم
Haihuwa Gabès (en) Fassara, 2 ga Yuni, 1921
ƙasa French protectorate of Tunisia (en) Fassara
Tunisiya
Mutuwa 1995
Makwanci Borgel cemetery (en) Fassara
Ƴan uwa
Abokiyar zama Georges Adda (en) Fassara
Yara
Sana'a
Sana'a Mai kare hakkin mata, gwagwarmaya da independence activist (en) Fassara
Imani
Jam'iyar siyasa Tunisian Communist Party (en) Fassara

Gladys Adda (1921 - 1995) 'yar kwaminisanci ce 'yar Tunisiya kuma mai fafutukar neman 'yancin kai da 'yancin mata.[1]

An haifi Adda a Gabes a ranar 2 ga watan Yuni shekara ta1921 a cikin dangin Yahudawa. Saɓanin yadda aka saba gani ta fara karatun ta da 'yan mata musulmai sannan ta haɗa kai.[1] Duk da cewa ta halarci azuzuwan firamare tare da ’yan matan Musulmi, Yahudawa, da Turawa, duk malamanta Faransawa ne ko Turawa; nuna wariyar launin fata da ba a ɓoyewa daga malaman Turai ta farkar da Adda game da mulkin mallaka na Turai. Al'ummarta yahudawa sun fuskanci wariyar launin fata daga 'yan tafarkin kin jinin Yahudu, amma al'ummar musulmi sun sami kariya.[2] Tana da shekara goma sha biyar ta auri wani mutum mai shekara bakwai kuma ta zauna da shi shekara bakwai har ta sake shi. A lokacin Tunusiya tana cikin daular Faransa sai dai lokacin yakin duniya na biyu lokacin da Jamus da Nazi ta mamaye ta. Adda ta tsunduma cikin fafutukar siyasa ta hanyar rarraba takardun adawa da Nazi da na mulkin mallaka a ɓoye a kan sojojin mamaya na Jamus a Vichy Tunisia.[2]

A shekarar 1944 ta haɗu kuma ta auri mijinta na biyu, Georges Adda, kuma sun haifi tagwaye. Ɗansu Serge Adda ya zama ɗan kasuwa na Faransa mai nasara. A wannan shekarar ita, Neila Haddad da Gilda khiari sun kasance masu kafa kungiyar Tarayyar Mata ta Tunisia (UFT). Wannan kungiya ce mai alaka da jam'iyyar gurguzu ta cikin gida kuma Nabiha Ben Miled wacce musulma ce ke jagoranta.[1] Ta shiga cikin shirya ɗakunan shan magani kyauta ga mata da madadin makarantun yara da manya. A lokacin an hana samun ilimi a makarantun mulkin mallaka sakamakon neman 'yancin kai na Tunisiya. Ana ganin Addas a matsayin haɗari kuma an tsare Georges a cikin shekarar 1950s. [2]

Ita da UFT na da hannu wajen shigar da ƙara ga mahukuntan Faransa a madadin fursunonin Tunisiya. Tunusiya ta sami 'yancin kai a shekara ta 1956 kuma ba kamar da yawa ita da mijinta sun yanke shawarar ci gaba da zama a Tunisiya ba, ita da UFT ba su wargaje ba kuma sun ba da goyon bayansu ga masu fafutuka a Aljeriya da ke kokarin samun 'yancin kai daga Faransa.[2] Adda da kawarta, sun shiga cikin fara rarraba jaridun Tunisiya kuma a sakamakon haka ta ba da laccoci a Tunis.

Gwauruwa Georges ta mutu a shekara ta 2009.[2]

  1. 1.0 1.1 1.2 Tunisian Women Yesterday and Today. Women of Tunisia, Weebly.com, Retrieved 26 March 2016
  2. 2.0 2.1 2.2 2.3 2.4 Professor Henry Louis Gates Jr.; Professor Emmanuel Akyeampong; Mr. Steven J. Niven (2 February 2012). Dictionary of African Biography. OUP USA. pp. 89–90. ISBN 978-0-19-538207-5.