Idrissa Timta

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Idrissa Timta
Emir of Gwoza (en) Fassara

Oktoba 1981 - 30 Mayu 2014
Rayuwa
Haihuwa 1942
ƙasa Najeriya
Mutuwa 30 Mayu 2014
Ƴan uwa
Yara
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Sana'a

Shehu Mustapha Idrissa Timta shi ne shugaban gargajiya na Najeriya wanda ya yi sarautar sarkin masarautar garin Gwoza, kuma shine sarki na uku a jerin sarakan masarautar, yayi mulki daga watan Oktoba shekarar 1981 har zuwa karshen rayuwarsa a watan Mayu shekarar 2014.[1] An kashe shi a wani hari da 'yan ta'addan ƙungiyar Boko Haram suka kai a ranar 30 ga watan Mayu, shekarar 2014.[1][2]

Farkon rayuwa da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haife shi a shekara ta 1942, ɗan Sarkin Gwoza na biyu, Idrisa Timta ne.[2] Ya halarci makarantar Muslim Elementary School, Gwoza, har zuwa shekara ta 1948 da babbar makarantar firamare a Bama, Nijeriya, daga shekarar 1952 zuwa shekarar 1960.[1] Sannan ya halarci Makarantar Sakandare ta Lardi (Government College Maiduguri) daga shekarar 1960 zuwa shekarar 1964.[1] Ya yi koyarwa na ɗan lokaci kaɗan sannan ya shiga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria inda ya karanci shari'a.[1] Timta ya fara aikinsa a matsayin mai duba kotunan yanki na tsohon tsarin shari'a na jihar Arewa maso Gabas.[1] An ƙara masa girma zuwa babban sufeto na kotunan yankin, muƙamin da ya riƙe har ya zama sarki a shekarar 1981.[2]

Sarauta[gyara sashe | gyara masomin]

An naɗa shi Sarki na 3 a garin Gwoza, karamar hukuma a Jihar Borno a yanzu, a watan Oktoba shekarar 1981.[1][2] An ɗaukaka Timta zuwa matsayin sarki na biyu a shekara ta 1987.[2] A watan Janairun shekarar 2014, Gwamnan Jihar Borno Kashim Shettima ya ƙara ɗaukaka matsayin sa, Sarkin mai sarautar gargajiya zuwa sarki mai daraja ta ɗaya.[1]

A ranar 13 ga watan Afrilu, shekara ta 2014, Timta ya yi Allah-wadai da ƙungiyar ta'addancin Boko Haram, wadda ke fafutuka a yankin Gwoza da sauran jihar Borno.[1] Ya yi tir da tashe-tashen hankula da tashin hankalin kungiyar da kuma mummunan tasirin zamantakewa da tattalin arziki da ta haifar a garin Gwoza.[2] A cikin jawabin Timta ya ce, “mutanenmu sun ga ƙaruwar hare-haren da ‘yan tada ƙayar bayan suka yi a cikin watanni huɗu da suka gabata. Hare-haren dai sun gurgunta rayuwar al'umma da na tattalin arziki a yankin baki ɗaya. . . Abin bakin ciki ne a ce maharan sun tare mutane na zuwa kasuwa, suna kashe mutane yadda suke so.[2] Timta ya roƙi gwamnatin Najeriya da ta kare kai hare-haren da ƙungiyar ta Boko Haram ke kaiwa.[2]

Dalilin mutuwa[gyara sashe | gyara masomin]

A ranar 30 ga watan Mayu, shekara ta 2014, Timta da wasu shugabannin gargajiya biyu suna tafiya zuwa jihar Gombe, Najeriya, don jana'izar Sarkin Gombe Shehu Abubakar, wanda ya rasu sakamakon cutar daji a ranar 27 ga watan Mayu.[1] Ƴan ta'addan Boko Haram ne suka kai wa ayarin motocin Timta hari a wani harin kwantan ɓauna da suka kai da karfe 9 na safe a hanyar Gombi-Garkida-Biu da ke kusa da Biu a Najeriya.[2][3] An kashe Timta ne a harin, tare da direbansa da ‘yan sanda biyu, waɗanda suka baiwa sauran sarakunan kariya a yayin harin kwantan ɓaunai.[1][2] Da kyar wasu sarakuna su biyu da suke tuki zuwa jana'izar tare da Timta - Sarkin Askira Abdullahi Ibn Muhammadu Askirama da Sarkin Uba Ali Ibn Ismaila Mamza II - suka tsallake rijiya da baya.[2][4]

Iyalan sa[gyara sashe | gyara masomin]

Ya rasu yana da shekaru 72 a duniya, ya bar mahaifiyarsa yar shekara ɗari da mata huɗu da ‘ya’ya ashirin da takwas.[2]

Sabon Sarki[gyara sashe | gyara masomin]

Masarautar Gwoza a jihar Borno ta naɗa magajinsa, Muhammad Timta, a matsayin Sarkin Gwoza na huɗu a watan Yunin shekarar 2014, makonni biyu bayan harin.[3] An gabatar wa sabon Sarki da takardar naɗi daga gwamnatin jihar Borno a ranar 13 ga watan Yuni, shekarar 2014.[3]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.00 1.01 1.02 1.03 1.04 1.05 1.06 1.07 1.08 1.09 1.10 Olanrewaju, Timothy (2014-06-01). "Tears as slain Emir of Gwoza is buried". The Sun (Nigeria). Archived from the original on 2014-06-11. Retrieved 2014-06-23.
  2. 2.00 2.01 2.02 2.03 2.04 2.05 2.06 2.07 2.08 2.09 2.10 2.11 Marama, Ndahi (2014-05-31). "Boko Haram attacks three Emirs, kills one". Vanguard (Nigeria). Retrieved 2014-06-23.
  3. 3.0 3.1 3.2 Otuchikere, Chika (2014-06-12). "Muhammad Timta Becomes New Emir Of Gwoza Tomorrow". Leadership (Nigeria). Retrieved 2014-06-23.
  4. "The Killing of the Emir of Gwoza". The Guardian (Nigeria). 2014-06-23. Archived from the original on 2014-06-24. Retrieved 2014-06-23.