Jump to content

Isaac Adomako-Mensah

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Isaac Adomako-Mensah
Member of the 2nd Parliament of the 1st Republic of Ghana (en) Fassara

9 ga Yuni, 1965 - 24 ga Faburairu, 1966
Election: 1965 Ghanaian parliamentary election (en) Fassara
Member of the 1st Parliament of the 1st Republic of Ghana (en) Fassara

1961 - 1965
Election: 1956 Gold Coast legislative election (en) Fassara
Member of the 2nd Parliament of the Gold Coast (en) Fassara

15 ga Yuni, 1954 - 17 ga Yuli, 1956
Election: 1954 Gold Coast legislative election (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa 1908
Mutuwa 23 Oktoba 1983
Karatu
Makaranta Achimota School Teachers' Training Certificate (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da Malami
Imani
Addini Kiristanci
Kirista
Jam'iyar siyasa Convention People's Party (en) Fassara

Isaac Joseph Adomako-Mensah (1908 - 1983) ɗan siyasan Ghana ne. Ya kasance ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Atwima Amansie daga shekarun 1954 zuwa 1956 da kuma daga shekarun 1961 zuwa 1965.[1] A shekarar 1965 ya zama ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Kwanwoma har zuwa shekara ta 1966.[2]

Rayuwar farko da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Adomako-Mensah a cikin shekarar 1908 a Akrofuom, Assin, yankin Ashanti. Ya yi karatunsa na farko a Makarantar St. Peter da ke Kumasi sannan ya tafi a shekarar 1925, bayan ya ci jarrabawar Standard Seven. Ya ci gaba a Achimota Training College inda ya kammala kwas ɗin sa a shekarar 1929. Daga baya ya yi karatu kuma ya ci jarrabawar kammala karatunsa na London.

Aiki da siyasa

[gyara sashe | gyara masomin]

Adomako-Mensah ya fara aiki a shekarar 1930 a matsayin malami mai aji na biyu. Ya yi koyarwa tun daga nan har zuwa shekara ta 1954 a lokacin da aka naɗa shi sakataren ilimi na ƙaramar hukumar Kumasi. A wannan shekarar ya shiga siyasa kuma ya tsaya takarar kujerar Atwima Amansie a tikitin Jam'iyyar Jama'a. [3] Ya ci zaɓe a zaɓen ‘yan majalisa na shekarar 1954 kuma ya kasance ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar daga ranar 15 ga watan Yuni 1954 zuwa 1956. Ya sha kaye a zaɓen 'yan majalisa na shekarar 1956 a hannun Joe Appiah duk da haka lokacin da aka kama Appiah a shekarar 1961 a ƙarƙashin dokar hana tsarewa ya karbi tsohon muƙaminsa na ɗan majalisa na mazaɓar Atwima Amansie. [4] A shekarar 1965 ya zama ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Kanwoma. Ya ci gaba da kasancewa a wannan matsayi har zuwa lokacin da aka kifar da gwamnatin Nkrumah a shekarar 1966.

Rayuwa ta sirri

[gyara sashe | gyara masomin]

Adomako-Mensah da matarsa Hannatu suna da 'ya'ya biyar. Ya kara haihuwa takwas da wasu mata. Ya mutu a ranar 23 ga watan Oktoba 1983.

  • Jerin 'yan majalisar da aka zaba a zaben majalisar dokokin Gold Coast na 1954
  • Jerin 'yan majalisar da aka zaba a zaben majalisar dokokin Gold Coast na 1956
  • Jerin sunayen 'yan majalisar da aka zaba a zaben 'yan majalisar dokokin Ghana na 1965
  1. "Ghana Year Book". Daily Graphic. 1964. p. 27.
  2. "Parliamentary Debates; Official Report, Part 2". Ghana National Assembly. 1965. p. iii.
  3. "Parliamentary debates : National Assembly official report". Government Printing Department (Publications Branch). Ghana Publications Corporation. 1964.
  4. "Parliamentary Debates; Official Report, Part 2". Ghana National Assembly: 266. 1962.