Jump to content

Joseph Utsev

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Joseph Utsev
Rayuwa
Haihuwa Jahar Benue, 1980 (45/46 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Jami'ar Najeriya, Nsukka
University of Agriculture, Makurdi (en) Fassara
Harsuna Turanci
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Joseph Utsev ɗan siyasan Kasar Najeriya ne wanda ya fito ne daga Karamar Hukumar Buruku ta Jihar Benue dake Najeriya . Wanda a yanzu shi ne Ministan albarkatun ruwa da kuma tsabtace Najeriya.[1]

Rayuwarsa ta farko da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Utsev a ranar 2 ga watan Disambar shekarar 1980 a Jihar Benue, Najeriya . Ya kammala karatu daga Jami'ar Aikin Gona ta Tarayya, dake Makurdi inda ya sami digiri na farko a fannin Injiniyanci, ya kammala karatu tare da girmamawa na biyu wato "Upper Division" a shekarar 2004. [2] Ya kuma sami digiri na biyu ,da kuma digiri na uku wato PhD a fannin albarkatun ruwa da injiniyan muhalli daga Jami'ar Najeriya, Nsukka a cikin shekarun 2007 zuwa 2011.[3][4]

Rayuwarsa na aiki

[gyara sashe | gyara masomin]

Shugaba Bola Tinubu ne ya nada Utsev a matsayin ministan albarkatun ruwa da tsabta, a jamhuriyar Tarayyar Najeriya. Joseph Utsev yakasance malami ne kuma farfesa.[5]

A cikin shekarar 2017, ya kuma yi aiki a matsayin kwamishinan Ma'aikatar Ruwa da kulla da Muhalli na Jihar Benue . [6]

A cikin shekarar 2024, Ƙungiyar Kare Ruwa ta Afirka wato (AWCP) ta amince da Utsev saboda jagorancinsa wajen sarrafa albarkatun ruwa, tabbatar da rarraba daidaito, da inganta ayyukan masu ɗorewa.[7]

  1. Okogba, Emmanuel (2024-06-20). "Utsev: Harnessing Nigeria's Water Resources For Economic Gains". Vanguard News (in Turanci). Retrieved 2025-04-01.
  2. Okogba, Emmanuel (2024-06-20). "Utsev: Harnessing Nigeria's Water Resources For Economic Gains". Vanguard News (in Turanci). Retrieved 2025-04-01.
  3. Orokpo, Treasure (2023-07-27). "Who is Joseph Utsev: Biography of Utsev, age, family, education, career". Idoma Voice Newspaper (in Turanci). Retrieved 2025-04-01.
  4. press_admin (2024-02-15). "Education Profile of Joseph Ustev". PressPayNg Blog (in Turanci). Retrieved 2025-04-01.
  5. Orokpo, Treasure (2023-07-27). "Who is Joseph Utsev: Biography of Utsev, age, family, education, career". Idoma Voice Newspaper (in Turanci). Retrieved 2025-04-01.
  6. Okogba, Emmanuel (2024-06-20). "Utsev: Harnessing Nigeria's Water Resources For Economic Gains". Vanguard News (in Turanci). Retrieved 2025-04-01.
  7. Reporter, Our (2024-10-24). "Minister of Water Resource Joseph Utsev bags award". The Nation Newspaper (in Turanci). Retrieved 2025-04-01.