Juliana Shonza
|
| |||
29 Oktoba 2015 - | |||
| Rayuwa | |||
| Haihuwa | 23 ga Afirilu, 1987 (38 shekaru) | ||
| ƙasa | Tanzaniya | ||
| Harshen uwa | Harshen Swahili | ||
| Karatu | |||
| Makaranta | Jami'ar Dar es Salaam | ||
| Harsuna |
Turanci Harshen Swahili | ||
| Sana'a | |||
| Sana'a | ɗan siyasa | ||
| Imani | |||
| Jam'iyar siyasa |
Party of the Revolution (en) | ||
Juliana Daniel Shonza (an haife ta a ranar 23 ga watan Afrilu 1987) 'yar siyasar ƙasar Tanzaniya ce kuma memba a jam'iyyar Chama Cha Mapinduzi (CCM) mai mulki.[1] Ita ce mataimakiyar ministar yaɗa labarai, al'adu, fasaha da wasanni a halin yanzu. Ta kasance ‘yar majalisa mai wa’adi ɗaya da aka naɗa a kujera ta musamman da aka keɓe a mata.[1]
Tarihi da ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Juliana Daniel Shonza a ranar 23 ga watan Afrilu 1987 a yankin Songwe. Ta kammala karatunta a Sakandaren Kibasila a shekarar 2005 da Dakawa a shekarar 2008. Digiri na farko a fannin zamantakewa daga shekarun 2008 zuwa 2011 da digiri na biyu akan ilimin zamantakewa daga shekarun 2013 zuwa 2015 daga Jami'ar Dar es Salaam da Jami'ar Dodoma.[1]
Aikin siyasa
[gyara sashe | gyara masomin]Shonza ta shiga harkar siyasa ne a lokacin da take Jami'ar Dar es Salaam a matsayin mataimakiyar shugabar majalisar matasan ƙasar Chadema ta ƙasa.[1] A shekarar 2013 ta koma Chama Cha Mapinduzi inda aka naɗa ta a matsayin mataimakiyar sakataren karfafa gwiwa a hedikwatar CCM.[1] A yayin babban zaɓen shekarar 2015, an naɗa Juliana Shonza a matsayin mamba a majalisar dokokin Tanzaniya ta hanyar kujerun mata na musamman don ajiyewa daga shekarun 2015 zuwa 2020.[ana buƙatar hujja][ <span title="This claim needs references to reliable sources. (October 2017)">abubuwan da ake bukata</span> ]
A cikin shekara ta 2017, an naɗa ta a matsayin mataimakiyar Minista a Ma'aikatar Watsa Labarai, Al'adu, Fasaha da Wasanni ta Shugaba John Magufuli a lokacin canje-canjen da ya yi a ranar 9 ga watan Oktoba 2017.[2] Tana aiki a majalisar ministoci ƙarƙashin Minista Dr. Harrison Mwakyembe.[3]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ 1.0 1.1 1.2 1.3 1.4 "JULIANA SHONZA : Nilihama Chadema baada ya kugundua Natumika". Mwananchinews (in Swahili). 29 November 2015. Retrieved 2017-10-09.CS1 maint: unrecognized language (link)
- ↑ "Tanzania: Efficiency Focused Reshuffle". Tanzania Daily News (Dar es Salaam). 2017-10-09. Retrieved 2017-10-09.
- ↑ Gerson Msigwa. "unveiled". Archived from the original on 2017-11-11. Retrieved 2017-10-09.