Justus Nyang'aya
![]() | |
| Rayuwa | |
| Haihuwa | Kenya, 1957 (68/69 shekaru) |
| ƙasa | Kenya |
| Karatu | |
| Makaranta |
University of London (en) |
| Sana'a | |
| Sana'a |
Mai kare ƴancin ɗan'adam da business executive (en) |
Justus Abonyo Nyang'aya kwararre ne a fannin ci gaban zamantakewa kuma mai fafutukar kare hakkin ɗan Adam[1][2] wanda ya yi aiki a matsayin kwamishina a hukumar zaɓe ta Kenya IEBC har zuwa ranar 2 ga watan Disamba shekara ta 2022.[3][4] Ya jagoranci kwamitin fasahar bayanai da sadarwa.
Yana ɗaya daga cikin kwamishinoni huɗu banda Juliana Cherera, Irene Masit, da Francis Wanderi waɗanda suka yi watsi[5] da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na Kenya a shekarar ta 2022[6][7][8] wanda shugaba Wafula Chebukati ya karanta.
Sana'a
[gyara sashe | gyara masomin]Justus Nyang`aya kwararre ne kan Ilimin Zaman Lafiya tare da UNESCO-PEER na tsawon shekara guda har zuwa shekara ta 1988 kafin ya zama mai ba da shawara kan ilimin 'yan gudun hijira a Windle Charitable Trust na tsawon watanni 27 daga watan Maris shekara ta 1988.
Ya kasance babban jami'in gudanarwa a Inter Sudanese Consultations on Peace & Justice (ISCOP) na tsawon shekara guda daga shekarun 2004. Daga tsakiyar shekarun 2009 ya yi aiki a matsayin Darakta[9] na Ƙasa na Amnesty International sama da shekaru takwas da rabi kafin ya ci gaba da zama babban jami’in gudanarwa a Leadership Education For Africa Development (LEAD Africa) a watan Janairu 2018 inda ya yi aiki na ƙasa da shekaru huɗu kafin a naɗa shi kwamishina a IEBC a ranar 2 ga watan Satumba 2021 kan cikakken lokaci.[10] Ya yi murabus a ranar 2 ga watan Disamba 2022.[11]
Ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]Justus ya yi matakinsa na 'A' a makarantar sakandare ta Kanunga da ke Kiambaa, gundumar Kiambu. Yana da Diploma a Jagoranci, Gudanar da Mulki, Zaman Lafiya da Canjin Rikici da Jagorancin Ƙungiya daga Jami'ar Majalisar Ɗinkin Duniya, (Jordan) da kuma Jagoran Fasaha (Ilimi) daga Cibiyar Ilimi, Jami'ar London.
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Nation,18 Dec 2013 Human rights defender Justus Nyang'aya shot in Rongai
- ↑ Business Daily Africa, 10 Mar 2016 The man who cares about your rights
- ↑ Standard, 2 Dec 2022 IEBC commissioner Justus Nyang'aya resigns amid probe
- ↑ The-Star, 2 Dec 2022 IEBC Commissioner Justus Nyang'aya resigns
- ↑ Citizen Digital, 17 Aug 2022 Justus Nyang’aya: Humanitarian Caught At The Centre Of IEBC Storm
- ↑ KDRTV, 17 Aug 2022 Little Known Details Of IEBC Commissioner Justus Nyang’aya Who Disputed Chebukati’s Presidential Results
- ↑ Whisper North, 18 Aug 2022 Justus Nyang’aya caught at the centre of IEBC storm Archived 2022-10-17 at the Wayback Machine
- ↑ Nation, 27 Aug 2022 Commissioner Nyang'aya: Foreigner, 3 IEBC staff accessed server and tampered with results
- ↑ Standard, 10 Mar 2013 Amnesty International Kenya director shot, wounded in Ongata Rongai
- ↑ Citizen Digital, 2 Sep 2021 Four New IEBC Commissioners Take Oath Of Office
- ↑ Nation, 2 Dec 2022 Justus Nyang’aya resigns as commissioner of IEBC
