Keketso Rantso
Appearance
| Rayuwa | |
|---|---|
| ƙasa | Lesotho |
| Sana'a | |
| Sana'a | ɗan siyasa da minista |
Keketso Rantso (ko Rantšo) minista ce a Lesotho. [1] Ta yi aiki a matsayin Ministan Kwadago da Aiki a Lesotho da aka naɗa a watan Yuni 2017. [2] [3]
Ilimi da aiki
[gyara sashe | gyara masomin]Rantso ta kammala karatun firamare a makarantar firamare ta Siloe. Ta samu satifiket dinta a Sakandare na Masentle da Diploma a fannin Kasuwanci da Diploma a fannin Sakatariya. An zaɓi Rantso a matsayin Mataimakiyar Sakatare na kungiyar Lesotho Congress for Democracy Youth League a shekarar 2003. A 2005, ta zama babbar sakatariya. Rantso ta wakilci Lesotho Congress for Democracy a shekarar 2012 kuma ta yi aiki a matsayin ministar ayyuka da sufuri. Ta riƙe muƙamai daban-daban a gwamnati kafin a naɗa ta ministar kwadago da samar da ayyukan yi. [2]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Mohloboli, Marafaele (2021-02-15). "Lesotho: Two Ministers Fired". allAfrica.com (in Turanci). Retrieved 2021-09-25.
- ↑ 2.0 2.1 "Honourable Keketso Rantšo". Government of Lesotho (in Turanci). 2018-11-19. Archived from the original on 2021-09-25. Retrieved 2021-09-25. Cite error: Invalid
<ref>tag; name ":0" defined multiple times with different content - ↑ "Minister of Labour and Employment of the Kingdom of Lesotho, Keketso Rantšo". www.ilo.org (in Turanci). Retrieved 2021-09-25.