Kungiyar Lauyoyi ta Gini Ikwatoriya
| Bayanai | |
|---|---|
| Iri |
association (en) |
Ƙungiyar lauyoyi ta Equatorial Guinea ( Colegio de Abogados de Guinea Ecuatorial ) ƙungiya ce ta lauyoyi ta ƙasar Equatorial Guinea. A watan Mayun 2002 gwamnatin ƙasar ta rushe ƙungiyar bisa doka. Ministan shari’a da kula da bauta ya kirkiro wata babbar majalisar lauyoyi, wanda shi da kansa ya ke jagorantar ta, ya kuma bayyana cewa dukkan lauyoyin wajibi ne ga masu son zama a ƙarƙashin ƙungiyar da su nemi hakan don zama mamba.[1]
Rahotanni
[gyara sashe | gyara masomin]Cibiyar kare hakkin dan Adam ta kungiyar lauyoyi ta kasa da kasa ta ziyarci kasar a watan Yulin 2003, kuma ta fitar da wani rahoto da ke nuna matukar damuwa. Sun bayar da misali da cin zarafi kamar azabtarwa, rashin tabbatar da yancin yin shari'a ta gaskiya, rashin 'yancin faɗar albarkacin baki da ƙungiyoyi, da kuma rashin kyawun yanayin gidan Yari ko Kaso. Sun kammala cewa ba a aiwatar da tsarin doka ba. [2] An kafa sabuwar ƙungiyar lauyoyi a watan Janairun 2003. Wani rahoto da aka shirya wa hukumar ta UNHCR da aka fitar a shekara ta 2004 ya bayyana dukkan mambobin sabuwar ƙungiyar lauyoyi an bayar da rahoton naɗa su, kuma suna karkashin kulawar Ministan Shari’a na ƙasar. [3]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "DISUELTO EL COLEGIO DE ABOGADOS DE GUINEA ECUATORIAL (THE BAR ASSOCIATION OF EQUATORIAL GUINEA DISSOLVED)". La Verdad (The Truth (454). February–July 2002. Archived from the original on 2011-06-09. Retrieved 2011-09-26.
- ↑ "Equatorial Guinea At the Crossroads". International Bar Association. October 2003. Archived from the original on 2012-03-29. Retrieved 2011-09-26.
- ↑ "ATTACKS ON JUSTICE - REPUBLIC OF EQUATORIAL GUINEA" (PDF). UNHCR. Retrieved 2011-09-26.