Kungiyar Ma'aikatan Gambiya
|
labor union (en) | |
| Bayanai | |
| Farawa | 1956 |
| Ƙasa | Gambiya |
Kungiyar Ma'aikatan Gambiya, ana takaita sunan ƙungiyar da (GWU), babbar ƙungiya ce a cikin ƙasar ta Gambiya.
Tarihi
[gyara sashe | gyara masomin]M.E. Jallow ne ya kafa GWU a shekarar 1956, Kuma shine Sakatare Janar na farko na ƙungiyar. Ƙungiyar ta yi rajista a hukumance a watan Yulin shekarar 1958. Da farko an shirya haɗa ma'aikatan ɓangaren gine-gine, ƙungiyar ta girma a ƙarshen shekarun 1950 bayan nasarorin da aka samu tare da ma'aikatan tashar jiragen ruwa waɗanda suka sami ingantaccen albashi da karin alawus.[1]::177 A shekara ta 1959, ƙungiyar ta haɗu da Kungiyar Kwadago ta Gambiya (GLU), kodayake an soke wannan gamin-bizar jim kaɗan bayan haka saboda bambance-bambance game da 'yancin kai da alaƙar ƙungiyar Kwadago ta Duniya.[2] A shekara ta 1977, gwamnatin ƙasar ta janye takardar izinin shaidar rajistar ƙungiyar bayan gazawar gabatar da asusun ƙungiyar ga gwamnatin.[1]:193
Dubi kuma
[gyara sashe | gyara masomin]- Alieu Ebrima Cham Joof
- Kungiyar Kwadago ta Bathurst
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ 1.0 1.1 Perfect, David (1986). "Organized Labour and Politics in The Gambia: 1960-85". Labour, Capital and Society / Travail, Capital et Société. 19 (2): 168–199. ISSN 0706-1706. JSTOR 43157755.
- ↑ Blackburn, Daniel, ed. (2016). Trade unions of the world (7th ed.). London: International Centre for Trade Union Rights. p. 192. ISBN 978-0-9933556-1-5.