Jump to content

Liberata Mulamula

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Liberata Mulamula
16. Minister of Foreign Affairs (en) Fassara

31 ga Maris, 2021 - 3 Oktoba 2022
Palamagamba John Aidan Mwaluko Kabudi (en) Fassara - Stergomena Lawrence Tax (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Yankin Kagera, 10 ga Afirilu, 1956 (70 shekaru)
ƙasa Tanzaniya
Harshen uwa Harshen Swahili
Karatu
Makaranta St. John's University (en) Fassara
Jami'ar Dar es Salaam
Harsuna Turanci
Harshen Swahili
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa, Mai wanzar da zaman lafiya da ambassador (en) Fassara
Kyaututtuka

Liberata Mulamula, ( née Rutageruka (an Haife ta a ranar 10 ga watan Afrilu 1956) jami'iyar diflomasiyar Tanzaniya ce kuma 'yar siyasa wacce ta yi aiki a matsayin Ministar Harkokin Waje da Haɗin gwiwar Gabashin Afirka daga shekarun Afrilu 2021 zuwa Oktoba 2022. Shugaba Samia Suluhu ce ta naɗa ta a ranar 31 ga watan Maris 2021 kuma aka rantsar da ita a ranar 1 ga watan Afrilu 2021. [1]

Ambasada Mulamula tana da tarihin fiye da shekaru 35 a matsayin jami'in diflomasiyya kuma mai gudanarwa a ma'aikatar harkokin waje da haɗin gwiwar yankin Tanzaniya, ciki har da jakadan Tanzaniya a Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York da Canada da kuma Amurka. [1]

Kafin ta yi ritaya daga aikin diflomasiyya a watan Afrilun 2016, ta yi aiki a matsayin babbar sakatariya a ma'aikatar harkokin waje da haɗin gwiwar ƙasashen gabashin Afirka na tsawon watanni bakwai, tsakanin watan Mayu 2015 zuwa Disamba 2015. [1]

Ta kuma yi aiki a matsayin Babbar Sakatariya na farko na Babban taron ƙasa da ƙasa kan yankin manyan tabkuna (ICGLR), wanda ke Bujumbura, Burundi, daga shekarun 2006 har zuwa 2011. A cikin wannan rawar, data taka ta kula da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a ƙasashe 11 na yankin manyan tabkuna na Afirka. [1]

Tarihi da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Liberata Rutageruka a cikin watan Afrilu 1956 a Misenyi, Kitobo Musibuka, gundumar Bukoba, a yankin Kagera. Tana da kanwa tagwaye mai suna Iluminata Maerere wacc ita ma ta yi hidimar UNDP seara Lion. Ta yi makarantar firamare a gida, tun tana shekara shida. Ta kammala karatunta na O-Level a Makarantar Mata ta Tabora a shekarar 1973. Ta ci gaba da kammala karatunta da kwatankwacin takardar shaidar kammala sakandare a Mzizima a shekarar 1975, bayan ta kammala karatunta na A-Level. [2]

Daga shekarun 1977 har zuwa 1980, Liberata ta yi karatu a Jami'ar Dar es Salaam, inda ta kammala karatunta na digiri na farko a fannin fasaha, inda ta karanci Kimiyyar Siyasa da Harkokin Duniya. Daga baya, ta sami digiri na biyu na Arts a cikin Gwamnati da Siyasa, daga Jami'ar St. John da ke Birnin New York, a cikin shekara ta 1989. Har ila yau, daga baya, Jami'ar St. [1] [2]

Yayin da Liberata jami'ar diflomasiyya ce ta aiki, ba ta shiga siyasa ba har sai da shugaba Jakaya Kikwete ya naɗa ta a matsayin babbar sakatariya a ma'aikatar harkokin waje a shekarar 2015. Bayan mutuwar shugaba John Magufuli ba zato ba tsammani, an naɗa ta a matsayin sabuwar ministar harkokin wajen ƙasar a ranar 31 ga watan Maris, 2021 a majalisar ministoci ta 6 ta Tanzania. Mulamula ta kasance a lokaci guda, a lokaci guda kuma an gabatar da ita ga majalisar dokokin Tanzaniya (2020-2025). [3]

Rayuwa ta sirri

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Liberata Rutageruka a ranar 10 ga watan Afrilun 1956 a Muleba, Bukoba, a yankin Kagera. [2] Ita ce mahaifiyar 'ya'ya biyu. [4]

  1. 1 2 3 4 5 Paul Owere (31 March 2021). "Liberata Mulamula, Tanzania's new foreign affairs Minister". Dar es Salaam. Archived from the original on 6 April 2021. Retrieved 5 April 2021.
  2. 1 2 3 Dar es Salaam University (2020). "Alumni of the Month: Liberata Rutageruka Mulamula, BA, MA: Year of Matriculation: 1977". University of Dar es Salaam. Archived from the original on 7 August 2020. Retrieved 5 April 2021.
  3. Paul Owere (1 April 2021). "President Samia reshuffles cabinet, drops chief secretary". Archived from the original on 2 April 2021. Retrieved 5 April 2021.
  4. UN Association of the National Capital Area (2020). "Ambassador Liberata Mulamula". UN Association of the National Capital Area. Archived from the original on 25 June 2021. Retrieved 5 April 2021.