Jump to content

Mama Fatima Singhateh

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Mama Fatima Singhateh
Minister of Justice (en) Fassara

12 ga Janairu, 2015 - 17 ga Janairu, 2017
Basiru Mahoney - Ba Tambadou (en) Fassara
Minister of Justice (en) Fassara

27 ga Augusta, 2013 - 27 ga Augusta, 2014 - Basiru Mahoney
Member of the National Assembly of Gambia (en) Fassara

Rayuwa
Haihuwa 20 century
ƙasa Gambiya
Karatu
Makaranta Jami'ar Hull
Sana'a
Sana'a lauya, ɗan siyasa da minista

Mama Fatima Singhateh (an Haife ta a ranar 1 ga watan Oktoba, 1974) lauya ce, alkaliya, kuma 'yar siyasa. [1] Tsakanin shekarun 2009 da 2013, ta kasance mai shari'a a babbar kotu, sannan a kotun ɗaukaka kara ta Gambia. [2] Daga baya ta zama ministar shari'a kuma babbar lauyan Gambia daga shekarun 2013 zuwa 2014, da kuma daga shekarun 2015 zuwa 2017. [3] [4] A halin yanzu tana aiki a matsayin mai ba da rahoto na Majalisar Ɗinkin Duniya na musamman kan siyar da cin zarafin yara. [5]

Rayuwar farko da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

Singhateh ta yi karatun farko da na sakandare a Banjul, Gambia. Ta sami digiri na LLB (Hons) daga Jami'ar Hull, United Kingdom a shekarar 1997, da Masters a Dokar Kasuwanci ta Duniya a can a shekarar 1998. Tsakanin shekarun 1998 zuwa 1999 ta kammala kwas ɗin koyar da sana'a a Jami'ar Wales kuma an kira ta zuwa Bar of England da Wales a matsayin Barrister.

Kafin naɗa ta a matsayin minista, Singhateh ta riƙe muƙamai da dama a cikin majalisar dokokin ƙasar Gambia a matsayin mai ba da shawara na jiha a shekarar 2002, a matsayin babbar mai ba da shawara na jiha, kuma a matsayin babbar mai ba da shawara. Tsakanin shekarun 2007 zuwa 2009 Singhateh ta shiga cikin kamfanoni masu zaman kansu, inda ta jagoranci sashin shari'a a wani banki na duniya. Daga nan aka naɗa ta alkaliya a babbar kotun ƙasar Gambia. [2]

Aikin shari'a

[gyara sashe | gyara masomin]

A watan Agustan 2009, bisa shawarar Hukumar Kula da Shari'a, Shugaba Yaya Jammeh ya naɗa Singhateh Alkaliyar Babbar Kotun. Daga nan aka ɗauke ta zuwa kotun ɗaukaka kara ta Gambia a shekarar 2012, inda ta yi aiki har zuwa lokacin da aka naɗa ta a matsayin ministar shari’a. A lokacin da take hidimar shari'a, ita ce mai kula da aikin na sashin shari'a na UNDP. [6]

Naɗin muƙamai na siyasa

[gyara sashe | gyara masomin]

A watan Agustan 2013 aka naɗa Singhateh a majalisar ministocin ƙasar Gambia domin ta riƙe muƙamin babbar mai shari'a kuma ministar shari'a. A lokacin ma'aikatarta an gyara wuraren ma'aikatar, [7] kuma an ƙaddamar da rajistar taga kasuwanci guda ɗaya. A cikin shekarar 2015 ma'aikatarta ta jagoranci gyare-gyare a cikin dokar laifuffukan jima'i, tare da haramta ayyukan yi wa mata kaciya a Gambia.[8] Shekara guda bayan haka, ta jagoranci yunkurin majalisa wanda ya haifar da haramta auren yara a cikin tarihi a Gambia. [9] [10] An sauke ta daga muƙamin ministar shari’a a watan Agustan 2014. A cikin watan Janairu 2015 an sake naɗa ta Babbar Atoni-Janar kuma Ministan Shari'a, [11] muƙamai da ta riƙe har zuwa ranar 17 ga watan Janairu 2017.

Wakiliyar Majalisar Ɗinkin Duniya na musamman kan sayar da yara da lalata da su

[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin watan Maris 2020, Majalisar Kare Hakkin Ɗan Adam ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta naɗa Singhateh mai ba da rahoto na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan tallace-tallace da cin zarafin yara, ta maye gurbin Maud de Boer-Buquicchio wanda ya riƙe muƙamin tun watan Mayu 2014. [12] [13]

  1. ""I Never Took Illegal Instructions from Jammeh," Says Mama Singhateh – Foroyaa Newspaper" (in Turanci). 2021-04-29. Retrieved 2024-12-11.
  2. 2.0 2.1 "Five Gambian Judges Appointed - Africa.gm - Africa news and information community". Archived from the original on 2 February 2017. Retrieved 28 December 2016.
  3. "Gambia's ruler names new justice minister after coup bid".
  4. "Gambia: Mama Fatima Singhateh Bounces Back". allAfrica.com. 14 January 2015. Retrieved 19 February 2017.
  5. "OHCHR | Special Rapporteur on the sale of children". www.ohchr.org. Retrieved 2020-05-06.
  6. "UNDP assists the Judiciary - Daily Observer". Archived from the original on 13 April 2016. Retrieved 28 December 2016.
  7. "Refurbished Justice Ministry building inaugurated - The Point Newspaper, Banjul, The Gambia". Retrieved 28 December 2016.
  8. Lyons, Kate (2015-11-24). "The Gambia bans female genital mutilation". The Guardian (in Turanci). ISSN 0261-3077. Retrieved 2020-05-06.
  9. "Gambia: Bill outlawing child marriage to become law". www.aa.com.tr. Retrieved 2020-05-06.
  10. "Ban on child brides becomes law in Gambia". eNCA (in Turanci). Archived from the original on 2022-01-29. Retrieved 2020-05-06.
  11. "Mama Fatima Singhateh bounces back - Daily Observer". Archived from the original on 13 April 2016. Retrieved 28 December 2016.
  12. "Where global solutions are shaped for you | News & Media | HUMAN RIGHTS COUNCIL ADOPTS UNIVERSAL PERIODIC REVIEW OUTCOME OF BOSNIA AND HERZEGOVINA, HOLDS DEBATE ON THE INTERNATIONAL DECADE FOR PEOPLE OF AFRICAN DESCENT, AND SUSPENDS ITS FORTY-THIRD SESSI". www.unog.ch. Retrieved 2020-05-06.
  13. nzoller (26 March 2020). "2020-03 UN HR Special Procedures: 19 Experts appointed during 43rd session by HR Council" (in Turanci). Retrieved 2020-05-06.