Musulunci da Dan Adam
|
Islamic term (en) | |
| Bayanai | |
| Addini | Musulunci da Sufiyya |
| Muhimmin darasi | ɗan adamtaka |
Koyarwan musulunci akan rayuwar Dan Adam da jindadin dan Adam: yana tsakiyar littafin nan da aka sani Qur"ani, wanda musulmai suka yarda maganar allah ne ga dukkan halittu. koyarwan ya Alakantu da abinda Annabi Muhammad yayi a zahirance ko ya koyar, zuwa ga Musulmai. Musulunci shine abinda Qur'ani ya bada umurni ayi da yadda Annabi ya bada umurni ayi ko ya aikata. duk wani fahimta ta Addinin akan wadannan abu biyu ne.
Walwalar jama'a a musulunci
[gyara sashe | gyara masomin]A cikin al’adar Musulunci, an gabatar da ra’ayin jin ƙai da taimakon jama’a a matsayin ɗaya daga cikin manyan ƙimominta, kuma an umurta da kuma ƙarfafa yin ayyukan hidimar jama’a ta hanyoyi daban-daban. Rayuwar addinin Musulmi ba ta cika ba idan ba a haɗa ta da hidima ga ɗan’adam ba. Wannan ayar daga Al-Qur’ani sau da yawa ake ambato don taƙaita ra’ayin Musulunci game da jin ƙai da taimakon jama’a.[1]
"Ba alheri ba ne ku juya fuskokinku zuwa gabas ko yamma; amma alheri shi ne wanda ya yi imani da Allah da Ranar Lahira, da mala’iku, da Littafi, da Manzanni; kuma ya kashe dukiyarsa – saboda ƙaunar Allah – ga 'yan'uwansa, da marayu, da mabukata, da matafiya, da masu roƙo, da kuma don 'yantar da bayi; ya tsai da salla,ya bayar da zakka; waɗanda suke cika alkawari idan suka ɗauka, kuma suke da haƙuri cikin wahala,da cuta da kuma lokacin tsanani. Waɗannan su ne masu gaskiya, kuma su ne masu tsoron Allah." (Quran 2:177).
haka kuma, an fayyace hakkoki ga iyaye, makwabta, dangi, marasa lafiya, tsofaffi, da ƙananan ƙungiyoyi a cikin Musulunci. A cikin wani dogon hadisi da aka rubuta a cikin Hadisin Qudsi (hadisin mai tsarki), an ce Allah, a Ranar Alƙiyama,zai ƙi yarda da waɗanda ba sa kulawa da marasa lafiya, da kuma waɗanda ba sa ba wa masu roƙo abinci. Allah zai tambaye su kuma Ya nemi bayani daga gare su. Wannan hadisin yana matsayin tunatarwa ga ɗan Adam dangane da wajibcin amsa kiran waɗanda ke cikin buƙata..[2] sai dai, wannan dole ne a aiwatar da shi cikin mafi kyawun hanya: kada a ci mutuncin kowa, kuma kada a jawo wata cuta ko barna daga hakan. A cikin al’adun Musulunci, iyali na da babban rawa da za ta taka wajen tarbiyyantar da ‘ya’yanta da koya musu ɗabi’u nagari domin su zama nagartattun ‘yan ƙasa. Gwamnati na da alhakin kare haƙƙin ɗan Adam ga ‘yan ƙasa. yayin da kungiyoyin farar hula da ba na gwamnti ba suke da rawar da zasu taka wajen gudanar da ayyukan jama'a da na jin kai.
Hakkokin Kungiyoyi Daban-daban a Musulunci
[gyara sashe | gyara masomin]Hakkokin Iyaye da Danginsu
A Musulunci, an ba da muhimmanci na musamman ga bautar iyaye da kuma hakkokinsu. Girmamawa da biyayya ga iyaye an mai da su wajibi na addini, kuma cin zarafinsu haramun ne a cikin fikihu da al'adun Musulunci. Dangane da hakkokin iyaye, umarnin Alƙur'ani shi ne a yi musu kyakkyawar mu'amala,a kula da su musamman lokacin tsufarsu.
- ↑ Corrigan, John; Denny, Frederick; Jaffee, Martin S (2016). Jews, Christians, Muslims: A Comparative Introduction to Monotheistic Religions. Routledge. p. 245. ISBN 9781317347002. Retrieved 22 January 2016.
- ↑ J. Cornell, Vincent (2007). Voices of Islam: Voices of life : family, home, and society. Greenwood Publishing Group. p. 129. ISBN 9780275987350.