Mutiu Shadimu
![]() | |||
---|---|---|---|
ga Afirilu, 2015 - District: Oshodi/Isolo I | |||
Rayuwa | |||
ƙasa | Najeriya | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa |
Mutiu Shadimu ɗan siyasan Najeriya ne kuma tsohon ɗan majalisar wakilan Najeriya mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Oshodi-Isolo I bayan ya zama zakara a zaɓen Najeriya na shekarar 2015 a watan Afrilu a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar People's Democratic Party. [1]
Ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]Mutiu ya halarci kwalejin Egba da ke Ilaro a jihar Ogun inda ya samu shaidar kammala karatunsa na babbar makarantar Afirka ta Yamma a shekarar 1985. Shi ma'aikaci ne a Cibiyar Kula da Haraji ta Najeriya da Cibiyar Haraji ta Najeriya.
Aiki da siyasa
[gyara sashe | gyara masomin]Kafin ya zama ɗan Majalisar Wakilai, ya kasance mai ba da shawara na Auditor, Tax and Management. A zaɓen shekarar 2015, ya tsaya takarar ɗan majalisar wakilai ta tarayya a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP kuma ya lashe zaɓen mazaɓar tarayya ta Oshodi-Isolo I. [2]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Nigeria, Media (2018-06-06). "Biography Of Mutiu Shadimu". Media Nigeria (in Turanci). Retrieved 2020-07-09.
- ↑ Ezeamalu, Ben (2019-02-25). "Agbaje berates INEC over late release of Lagos election results" (in Turanci). Retrieved 2020-07-09.