Jump to content

Nassir Ali Ahmed

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Nassir Ali Ahmed
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya,

11 ga Yuni, 2019 -
District: Nasarawa
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya,

Rayuwa
Haihuwa 1968 (57/58 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Nassir Ali Ahmed dan siyasa daga jihar Kano a Najeriya ya taba zama wakilin mazabar Nassarawa a majalisar dokokin kasar. An zabe shi a matsayin dan majalisar wakilai a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kuma ya rike mukamin daga 2011 zuwa 2015, 2015 zuwa 2019, da 2019 zuwa 2023.[1]

Rayuwar farko da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Ahmed a ranar 2 ga Yuni, 1968, a karamar hukumar Nasarawa ta jihar Kano, Najeriya. Ya fara karatunsa a shekarar 1973 a Kano Capital School inda ya kammala a shekarar 1980, inda ya samu shaidar kammala karatunsa na farko (FSLC). Ya samu shaidar kammala karatunsa na Senior School a shekarar 1986 a Kwalejin Gwamnatin Tarayya ta Kano. Daga nan Ahmed ya samu shaidar difloma a fannin lissafi a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, sannan ya yi digiri na farko a fannin lissafi a Jami’ar Jos a shekarar 1992. A shekarar 1993 ya samu digirin MBA a Jami’ar Bayero ta Kano. Ya yi aiki a matsayin mataimakin shugaban kwamitin abun ciki na gida.[2][3]

Sana'ar siyasa

[gyara sashe | gyara masomin]

Ahmed ya zama wakilin mazabar tarayya ta Nassarawa a majalisar wakilai ta kasa tsawon wa'adi uku a jere: daga 2011 zuwa 2015, 2015 zuwa 2019, da 2019 zuwa 2023. An zabe shi a matsayin dan majalisar wakilai a karkashin jam'iyyar All Progressives Congress (APC).[4]

  1. Citizen Science Nigeria". citizensciencenigeria.org. Retrieved 2025-01-05
  2. Hon. Nassir Ali biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2025-01-05.
  3. 2022: Hon. Nasir Ali Ahmed emerges constituency development Icon of the year award winner - SolaceBase". 2022-12-15. Retrieved 2025-01-05
  4. "undefined candidate data for 2023 - Stears Elections". www.stears.co. Retrieved 2025-01-05