Neneh MacDouall-Gaye
![]() | |||
5 ga Janairu, 2015 - 16 ga Janairu, 2017 ← Bala Garba Jahumpa - Ousainou Darboe (en) | |||
| Rayuwa | |||
| Haihuwa | Banjul, 8 ga Afirilu, 1957 (68 shekaru) | ||
| ƙasa | Gambiya | ||
| Sana'a | |||
| Sana'a | ɗan siyasa, Mai wanzar da zaman lafiya da minista | ||
Neneh MacDouall-Gaye (an haife ta a ranar 8 ga watan Afrilu 1957) 'yar siyasar ƙasar Gambia ce kuma jami'iyar diflomasiyya.[1] Ta riƙe muƙamin ministar harkokin wajen Yahya Jammeh na ƙarshe daga shekarar 2015 zuwa 2017 da kuma matsayin jakadiyar Gambia a Amurka a shekarar 2009.[2]
Rayuwar farko da ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi MacDouall-Gaye a Banjul kuma ta halarci makarantar sakandare ta St Joseph, inda ta kammala a shekarar 1974. Daga nan sai ta sami difloma a fannin sadarwar jama'a daga Cibiyar Horar da Rediyo da Talabijin, wani bangare na ginin gidan talabijin na Maspero a Alkahira, Masar, a cikin shekarar 1980.[3]
Aikin siyasa
[gyara sashe | gyara masomin]Da farko MacDouall-Gaye 'yar jarida ce, inda ta shiga Rediyon Gambia a shekarar 1979. Ta sami magoya baya da yawa saboda 'golden voice'.[4]
An naɗa MacDouall-Gaye a matsayin Sakatariyar Harkokin Kasuwanci, Masana'antu da Ayyuka a cikin shekarar 2005, matsayin da ta riƙe na 'yan watanni. Daga nan aka naɗa ta a matsayin Sakatariyar Harkokin Sadarwa da Fasahar Watsa Labarai ta Gwamnati, ta yi aiki har zuwa 19 ga watan Maris 2008,[5] lokacin da Fatim Badjie ta maye gurbinta.[6] An sanar da cewa za ta zama wakiliyar Gambia ta dindindin a Majalisar Ɗinkin Duniya, amma a maimakon haka, an naɗa Susan Waffa-Ogoo a matsayin.[7]
An naɗa MacDouall-Gaye a matsayin Manajin Darakta na Kamfanin Observer Ltd, mawallafin The Daily Observer, a ranar 19 ga watan Yuni 2008. Ta maye gurbin Dida Halake, wacce a lokacin take tsare a ofishin ‘yan sanda na Kotu.[8] MacDouall-Gaye ta riƙe wannan muƙamin har zuwa lokacin da aka naɗa ta a matsayin Jakadiyar Gambia a Amurka a ranar 30 ga watan Janairun 2009. A lokaci guda kuma an naɗa Musa Mbob, tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda a matsayin mataimakin jakada a Amurka. An dakatar da muƙaminta na Jakadiya a ranar 12 ga watan Agusta 2009.[9]
A ranar 5 ga watan Janairu 2015, an naɗa MacDouall-Gaye a matsayin Ministan Harkokin Waje, ta maye gurbin Bala Garba Jahumpa.[10] A ranar 16 ga watan Janairun 2017, yayin rikicin tsarin mulkin Gambia na shekarar 2016-2017, MacDouall-Gaye ta fitar da wasikar murabus ɗin ta ga shugaban ƙasar Gambia Yahya Jammeh.[11]
Duba kuma
[gyara sashe | gyara masomin]- Jerin sunayen ministocin harkokin waje a shekarar 2017
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "Mrs. Neneh MacDouall-Gaye". State House. Archived from the original on 13 March 2017. Retrieved 13 March 2017.
- ↑ "Mrs. Neneh MacDouall-Gaye". State House. Archived from the original on 13 March 2017. Retrieved 13 March 2017.
- ↑ "Mrs. Neneh MacDouall-Gaye". State House. Archived from the original on 13 March 2017. Retrieved 13 March 2017.
- ↑ "Neneh Macdouall is Gambia's New Ambassador to US". The Point. 30 January 2009. Retrieved 10 February 2017.
- ↑ "Neneh Macdouall-Gaye's Appointment Terminated". The Point. 12 August 2009. Retrieved 10 February 2017.
- ↑ Arnold Hughes; David Perfect (11 September 2008). Historical Dictionary of The Gambia. Scarecrow Press. ISBN 978-0-8108-6260-9.
- ↑ "Susan Waffa Ogoo is Gambia's New UN Rep". The Point. 21 April 2008. Retrieved 10 February 2017.
- ↑ "Neneh Macdouall Gaye is Daily Observer New Boss". The Point. 16 June 2008. Retrieved 10 February 2017.
- ↑ "Neneh Macdouall Gaye is Daily Observer New Boss". The Point. 16 June 2008. Retrieved 10 February 2017.
- ↑ "MacDouall-Gaye appointed Foreign Affairs Minister, Sheriff Bojang Information". The Point. 6 January 2015. Retrieved 10 February 2017.
- ↑ "Gambia's Foreign Minister Resigns Leaving Yahya Jammeh With One Less Ally". Answers Africa. 17 January 2017. Retrieved 10 February 2017.
