Nusura Tiperu
![]() | |||
---|---|---|---|
| |||
Rayuwa | |||
Haihuwa |
Yumbe (en) ![]() | ||
ƙasa | Uganda | ||
Mazauni |
Arusha (en) ![]() | ||
Karatu | |||
Makaranta | Jami'ar Makerere | ||
Harsuna | Turanci | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa | ||
Imani | |||
Addini | Musulunci |
Ambasada Nusura TIPERU jami'ar diflomasiyar Uganda ce, kuma 'yar siyasa ce mai gogewa a matsayin 'yar majalisar dokoki ta ƙasa da gabashin Afirka. Ta yi aiki a matsayin 'yar Majalisar Matasa ta Mata ta farko a Uganda bayan fitar da Kundin Tsarin Mulki na shekarar 1995.
Daga shekarun 2001 zuwa 2006, an zaɓe ta don wakiltar matan Yumbe a Majalisar Dokokin Uganda kuma ta kasance mai taka rawa wajen tabbatar da zaman lafiya a Arewacin Uganda. Ita ce mai neman zaman lafiya.
Daga watan Yuni 2007 zuwa Yuni 2017, Ambasada Tiperu ta yi wa'adi biyu a jere a matsayin ɗaya daga cikin membobi tara da ke wakiltar Uganda a majalisar dokoki ta 2 da ta 3 ta Gabashin Afirka (EALA) a Arusha, Tanzania; hedkwatar wannan majalisa.
An zaɓe ta ne domin ta wakilci gwamnatin Jamhuriyar Uganda a matsayin ɗaya daga cikin majalisar wakilan jami'ar Musulunci ta ƙasar Uganda. Jami'ar da ke da alaka da kungiyar haɗin kan ƙasashen musulmi (OIC) da ke ƙasar Uganda.
An naɗa Tiperu a matsayin Jakadiyar Uganda a Turkiye a cikin watan Disamba 2021. [1]
Tarihi da ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]An haife ta a gundumar Yumbe, yankin Yammacin Nil, a Arewacin Uganda a ranar 21 ga watan Oktoba 1974. Nusura Tiperu ta halarci makarantar Mukono Town Academy a gundumar Mukono don karatunta na A-Level, daga shekarun 1992 har zuwa 1993. Daga nan ta shiga Jami'ar Makerere, babbar jami'a a Uganda, inda ta karanci ilimin zamantakewa daga shekarun 1994 zuwa 1997. Ta kammala karatun digiri na farko a fannin ilimin zamantakewa. [2]
Sana'a
[gyara sashe | gyara masomin]Daga shekarun 1996 har zuwa 2001, ta yi aiki a matsayin 'yar Majalisar Matasa ta Mata, wacce ke wakiltar dukkan mata matasa a Uganda. Daga nan aka zaɓe ta ta zama ‘yar majalisa mace, mai wakiltar gundumar Yumbe a majalisar daga shekarun 2001 zuwa 2006. Daga shekarun 2007 zuwa 2012, ta yi aiki a Majalisar Dokokin Gabashin Afirka a Arusha, Tanzania, mai wakiltar Jamhuriyar Uganda. A watan Yunin 2012, an sake zaɓen ta don yin aiki iri ɗaya na wani wa'adin shekaru biyar. [3]
Sauran nauyi
[gyara sashe | gyara masomin]Nusura Tiperu Omar mamba ce a tarihin kwamitin tsakiya na National Resistance Movement, jam'iyyar siyasa mai mulki a Uganda tun a shekarar 1986. [4] Ita ce kuma shugabar kungiyar mata musulmi ta duniya. Mahaifiyar 'ya'ya uku ce; 'yan mata biyu da namiji ɗaya. [3] Tana iya magana da harsuna kamar haka: Turanci, Swahili, Alur, Aringa da Luganda. Daga shekarun 2012 zuwa 2015, ta yi aiki a matsayin mamba a Hukumar EALA. Hukumar "tana tafiyar da al'amuran Majalisar, tana tsara harkokin kasuwanci da shirye-shiryen majalisar, da kuma naɗa mambobin sauran kwamitoci." [5]
Duba kuma
[gyara sashe | gyara masomin]- Al'ummar Gabashin Afirka
- Majalisar Uganda
- Margaret Zziwa
- Daniel Kidega
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Job Bwire (12 December 2022). "Nusura Tiperu sent to Ankara as Museveni appoints new ambassadors". Daily Monitor. Retrieved 21 October 2022.
- ↑ S.D. Kafeero (20 November 2018). "Government names 14 on constitutional review team". Daily Monitor. Retrieved 21 October 2022.
- ↑ 3.0 3.1 Namutebi, Joyce (2012). "Uganda's EALA MPs for 2012–2017". Archived from the original on 17 February 2015. Retrieved 16 February 2015. Cite error: Invalid
<ref>
tag; name "Re-elected" defined multiple times with different content - ↑ "Zziwa, Tiperu, Nankabirwa Face Bitamazire". 3 September 2010. Archived from the original on 17 February 2015. Retrieved 16 February 2015.
- ↑ Karuhanga, James (20 January 2015). "EALA Elects New Commission Members". Retrieved 16 February 2015.