Jump to content

Nusura Tiperu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Nusura Tiperu
Member of the Parliament of Uganda (en) Fassara

Rayuwa
Haihuwa Yumbe (en) Fassara, 21 Oktoba 1974 (50 shekaru)
ƙasa Uganda
Mazauni Arusha (en) Fassara
Karatu
Makaranta Jami'ar Makerere
Harsuna Turanci
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Addini Musulunci

Ambasada Nusura TIPERU jami'ar diflomasiyar Uganda ce, kuma 'yar siyasa ce mai gogewa a matsayin 'yar majalisar dokoki ta ƙasa da gabashin Afirka. Ta yi aiki a matsayin 'yar Majalisar Matasa ta Mata ta farko a Uganda bayan fitar da Kundin Tsarin Mulki na shekarar 1995.

Daga shekarun 2001 zuwa 2006, an zaɓe ta don wakiltar matan Yumbe a Majalisar Dokokin Uganda kuma ta kasance mai taka rawa wajen tabbatar da zaman lafiya a Arewacin Uganda. Ita ce mai neman zaman lafiya.

Daga watan Yuni 2007 zuwa Yuni 2017, Ambasada Tiperu ta yi wa'adi biyu a jere a matsayin ɗaya daga cikin membobi tara da ke wakiltar Uganda a majalisar dokoki ta 2 da ta 3 ta Gabashin Afirka (EALA) a Arusha, Tanzania; hedkwatar wannan majalisa.

An zaɓe ta ne domin ta wakilci gwamnatin Jamhuriyar Uganda a matsayin ɗaya daga cikin majalisar wakilan jami'ar Musulunci ta ƙasar Uganda. Jami'ar da ke da alaka da kungiyar haɗin kan ƙasashen musulmi (OIC) da ke ƙasar Uganda.

An naɗa Tiperu a matsayin Jakadiyar Uganda a Turkiye a cikin watan Disamba 2021. [1]

Tarihi da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

An haife ta a gundumar Yumbe, yankin Yammacin Nil, a Arewacin Uganda a ranar 21 ga watan Oktoba 1974. Nusura Tiperu ta halarci makarantar Mukono Town Academy a gundumar Mukono don karatunta na A-Level, daga shekarun 1992 har zuwa 1993. Daga nan ta shiga Jami'ar Makerere, babbar jami'a a Uganda, inda ta karanci ilimin zamantakewa daga shekarun 1994 zuwa 1997. Ta kammala karatun digiri na farko a fannin ilimin zamantakewa. [2]

Daga shekarun 1996 har zuwa 2001, ta yi aiki a matsayin 'yar Majalisar Matasa ta Mata, wacce ke wakiltar dukkan mata matasa a Uganda. Daga nan aka zaɓe ta ta zama ‘yar majalisa mace, mai wakiltar gundumar Yumbe a majalisar daga shekarun 2001 zuwa 2006. Daga shekarun 2007 zuwa 2012, ta yi aiki a Majalisar Dokokin Gabashin Afirka a Arusha, Tanzania, mai wakiltar Jamhuriyar Uganda. A watan Yunin 2012, an sake zaɓen ta don yin aiki iri ɗaya na wani wa'adin shekaru biyar. [3]

Sauran nauyi

[gyara sashe | gyara masomin]

Nusura Tiperu Omar mamba ce a tarihin kwamitin tsakiya na National Resistance Movement, jam'iyyar siyasa mai mulki a Uganda tun a shekarar 1986. [4] Ita ce kuma shugabar kungiyar mata musulmi ta duniya. Mahaifiyar 'ya'ya uku ce; 'yan mata biyu da namiji ɗaya. [3] Tana iya magana da harsuna kamar haka: Turanci, Swahili, Alur, Aringa da Luganda. Daga shekarun 2012 zuwa 2015, ta yi aiki a matsayin mamba a Hukumar EALA. Hukumar "tana tafiyar da al'amuran Majalisar, tana tsara harkokin kasuwanci da shirye-shiryen majalisar, da kuma naɗa mambobin sauran kwamitoci." [5]

  • Al'ummar Gabashin Afirka
  • Majalisar Uganda
  • Margaret Zziwa
  • Daniel Kidega
  1. Job Bwire (12 December 2022). "Nusura Tiperu sent to Ankara as Museveni appoints new ambassadors". Daily Monitor. Retrieved 21 October 2022.
  2. S.D. Kafeero (20 November 2018). "Government names 14 on constitutional review team". Daily Monitor. Retrieved 21 October 2022.
  3. 3.0 3.1 Namutebi, Joyce (2012). "Uganda's EALA MPs for 2012–2017". Archived from the original on 17 February 2015. Retrieved 16 February 2015. Cite error: Invalid <ref> tag; name "Re-elected" defined multiple times with different content
  4. "Zziwa, Tiperu, Nankabirwa Face Bitamazire". 3 September 2010. Archived from the original on 17 February 2015. Retrieved 16 February 2015.
  5. Karuhanga, James (20 January 2015). "EALA Elects New Commission Members". Retrieved 16 February 2015.