Ofishin Rediyo da Talabijin na Nijar
| Bayanai | |
|---|---|
| Iri |
ginin daji da broadcaster (en) |
| Ƙasa | Nijar |
| Aiki | |
| Kayayyaki | |
| Mulki | |
| Hedkwata | Niamey |
| Tsari a hukumance |
state-owned enterprise (en) |
| Mamallaki | Nijar |
| Tarihi | |
| Ƙirƙira | 11 ga Faburairu, 1967 |
| Founded in | Niamey |
| ortn.ne | |

Gidan Rediyon Talabijin na Nijar (RTN), wanda aka fi sani da Ofishin Rediyo da Talabijin na Nijar (Faransanci: Office de radiodiffusion et Télévision du Niger), ko ORTN a takaice, shine gidan da ake watsa shirye-shiryen jihar na ƙasar Yammacin Afirka na Nijar. RTN na aiki da tashar talabijin ta Télé Sahel, gidan rediyo na Voix du Sahel, da kuma tashar tauraron dan adam ta Tal TV (2001). Ma'aikatar Al'adu, Fasaha da Sadarwa ce ke kula da RTN kuma tana tallafawa gidan.
Tarihi
[gyara sashe | gyara masomin]A ranar 11 ga watan Fabrairu 1967, an haɗe/maja na ayyukan gidan Rediyon da Talabijin zuwa ORTN.
A watan Afrilun shekarar 2000, an ba da izinin watsa shirye-shirye gaba ɗaya kuma a sakamakon haka an kafa tashoshin talabijin masu zaman kansu da yawa a Nijar. ORTN ta mayar da martani ga wannan ci gaba ta hanyar kirkirar shirin talabijin na biyu: Tal TV ta fara watsa shirye-shirye tun a shekarar 2001.
ORTN ta tura biyu daga cikin mambobi bakwai zuwa Conseil de Presse (Majalisar Labarai) tun lokacin da aka kafa ta a watan Maris na shekara ta 2007. Wannan ma'aikatar kula da kanta ta ƙafofin watsa labarai na Nijar ta kafa kanta aikin saka idanu kan ka'idojin ayyukan ƙafofin watsa labarai kuma tana da alhakin bayar da katunan shaidar aiki ga ɗan jarida ko manema labarai.[1]
A watan Afrilu na shekara ta 2022, ta zama Rediyo Télévision du Niger don raba ayyukan edita daga ayyukan watsa shirye-shiryen da aka yi a sabuwar tashar Télédiffusion du Niger (TDN).
Sanarwar hukumar gwamnatin game da juyin mulkin soja na 2023 da Janar Abdourahamane Tchiani ya yi an ayyana hakan ne daga tashar ta RTN Télé Sahel.[2]
RTN memba ne na Ƙungiyar watsa shirye-shiryen Afirka (AUB).[3]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Idrissa, Rahmane (2012). Historical dictionary of Niger. Samuel Decalo (4th ed.). Lanham, MD: Scarecrow Press. ISBN 978-0-8108-6094-0. OCLC 773278542.
- ↑ "EU rejects Niger coup authorities, cuts aid – DW – 07/29/2023". dw.com (in Turanci). Retrieved 2023-08-30.
- ↑ "Ours members". AUB-UAR MOBILE APP (in Turanci). Retrieved 2023-08-30.