Pape Seydou N'Diaye

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Pape Seydou N'Diaye
Rayuwa
Haihuwa Dakar, 11 ga Faburairu, 1993 (31 shekaru)
ƙasa Senegal
Karatu
Harsuna Faransanci
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
  Senegal national association football team (en) Fassara-
 
Muƙami ko ƙwarewa Mai tsaran raga

Pape Seydou N'Diaye (an haife shi ranar 11 ga watan Fabrairun 1993) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne kuma ɗan ƙasar Senegal wanda a halin yanzu yake taka leda a matsayin mai tsaron gida a kulob ɗin Danish 2nd Division Jammerbugt FC.

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Kulob[gyara sashe | gyara masomin]

Tun 2012 N'Diaye ya taka leda a ASC Niarry Tally.

A ranar 3 ga watan Nuwamban 2021, N'Diaye ya shiga kulob ɗin Danish 1st Division Jammerbugt FC kan yarjejeniya har zuwa cikin watan Yunin 2023. [1]

Ƙasashen Duniya[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan zaɓen da aka yi masa na gasar Olympics, N'Diaye ya halarci gasar cin kofin nahiyar Afirka na ƴan ƙasa da shekaru 23 na 2015 a ƙasarsa ta haihuwa. Senegal ce ta zo ta huɗu a gasar bayan ta sha kashi a hannun Najeriya a wasan kusa da na ƙarshe da kuma wasan ƙarshe a matsayi na uku a hannun Afirka ta Kudu .

N'Diaye ya buga wasansa na farko a babbar tawagar Senegal a ranar 10 ga watan Fabrairun 2016, a wasan sada zumunci da suka doke Mexico da ci 2-0 a Miami. [2] Ya halarci gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2017 da aka yi a Gabon.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. JAMMERBUGT FC HENTER KEEPER FORSTÆRKNING Archived 2022-01-28 at the Wayback Machine, jammerbugtfc.dk, 3 November 2021
  2. Pape Seydou N'Diaye at national-football-teams.com

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]

  • Pape Seydou N'Diaye at WorldFootball.net
  • Pape Seydou N'Diaye at FootballDatabase.eu