Ross Wilson (mai kula da kwallon kafa)
| Rayuwa | |
|---|---|
| Haihuwa | 4 Mayu 1984 (41 shekaru) |
| Sana'a | |
| Sana'a | ɗan kasuwa |
Ross Wilson (an haife shi a ranar 4 ga Mayu 1984) shi ne babban jami'in kwallon kafa na Scotland wanda shine Daraktan Wasanni na Newcastle United Football Club .
Rayuwa ta farko
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Wilson a ranar 4 ga Mayu 1984 a Falkirk, Scotland kuma ɗan asalin Larbert ne, Scotland . Yayinda yake girma, ya goyi bayan kungiyar Falkirk FC ta Scotland kuma ya halarci Jami'ar Strathclyde a Scotland.[1]
Ayyuka
[gyara sashe | gyara masomin]Wilson ya yi aiki a matsayin kocin matasa na kungiyar Ingila ta Watford FC . Bayan ya kasance a can, an nada shi a matsayin kocin matasa na kungiyar Falkirk FC ta Scotland a shekarar 2010. A lokacin rani na shekara ta 2012, an nada shi darektan ayyukan kwallon kafa na kungiyar Huddersfield Town AFC ta Ingila.
Kafin kakar 2015-16, an nada shi darektan ayyukan kwallon kafa na kungiyar Southampton FC ta Ingila. Shekaru hudu bayan haka, an nada shi darektan wasanni na Rangers FC na Scotland, inda ya taimaka wa kulob din ya lashe gasar.[2] Daga baya, an nada shi darektan wasanni na kungiyar Nottingham Forest FC ta Premier League ta Ingila.[3]
A ranar 11 ga Oktoba 2025, Newcastle United FC ta ba da sanarwar nadin Ross Wilson a matsayin Daraktan Wasanni na Kungiyar. [4]
manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "Who is Rangers' new director of football Ross Wilson?" (in Turanci). Falkirk Herald. 24 October 2019. Retrieved 28 July 2025.
- ↑ "Who is Rangers' new director of football Ross Wilson?" (in Turanci). Falkirk Herald. 24 October 2019. Retrieved 28 July 2025.
- ↑ "Who is Rangers' new director of football Ross Wilson?" (in Turanci). Falkirk Herald. 24 October 2019. Retrieved 28 July 2025.
- ↑ "Who is Rangers' new director of football Ross Wilson?" (in Turanci). Falkirk Herald. 24 October 2019. Retrieved 28 July 2025.