Jump to content

Saeed Gul

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Saeed Gul
Rayuwa
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Jamiat Ulema-e-Islam (en) Fassara

Saeed Gul ɗan siyasan Pakistan ne wanda ya taɓa zama memba a majalisar lardin Khyber Pakhtunkhwa, daga watan Mayun shekarar 2013 zuwa Mayun shekara ta 2018. A baya ya kasance memba na majalisar lardin Khyber Pakhtunkhwa daga shekarar 2002 zuwa 2007.

Yana da digiri na Master of Arts.[1]

Sana'ar siyasa

[gyara sashe | gyara masomin]

An zaɓe shi ɗan majalisar dokokin lardin arewa maso yamma a matsayin ɗan takarar Muttahida Majlis-e-Amal daga mazaɓar PF-96 (Lower Dir-III) a babban zaɓen Pakistan na shekarar 2002. Ya samu ƙuri'u 10,326 sannan ya doke Ɗan takarar jam'iyyar Pakistan Peoples Party (PPP). [2]

An sake zaɓe shi a Majalisar lardin Khyber Pakhtunkhwa a matsayin ɗan takarar Jamaat-e-Islami Pakistan daga Mazaɓar PK-96 (Lower Dir-III) a babban zaɓen Pakistan na 2013 . Ya samu ƙuri'u 14,193 sannan ya doke dan takarar jam'iyyar PPP. [3]

  1. "Profile". www.pakp.gov.pk. KP Assembly. Archived from the original on 7 June 2017. Retrieved 15 January 2018.
  2. "2002 election result" (PDF). ECP. Archived from the original (PDF) on 26 January 2018. Retrieved 30 April 2018.
  3. "2013 election result" (PDF). ECP. Archived from the original (PDF) on 1 February 2018. Retrieved 29 April 2018.