Jump to content

Sarah Kachingwe

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Sarah Kachingwe
Rayuwa
Haihuwa Rusape (en) Fassara, 1936
ƙasa Zimbabwe
Mutuwa 2012
Karatu
Makaranta University of Zimbabwe (en) Fassara
University of London (en) Fassara
Goromonzi High School (en) Fassara
Harsuna Turanci
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da gwagwarmaya
Wurin aiki Zimbabwe

Sarah Kachingwe (née Chavunduka; [1] 1936–2012) 'yar siyasa ce kuma ‘yar gwagwarmayar Zimbabwe. Ita ce bakar fata ta farko da ta yi rajista a Kwalejin Jami'ar Rhodesia a shekarar 1957. Ta ci gaba da zama sakataren yaɗa labarai, wasiku da sadarwa sannan kuma ta yi aiki a hukumar Zimpapers da hukumar kula da gandun daji. [2]

Tarihin Rayuwa

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Kachigwe a Rusape, Zimbabwe, a cikin shekarar 1936. [2] Ta halarci makarantar sakandare ta Goromonzi. A cikin shekarar 1957 ta shiga Jami'ar Kwalejin Rhodesia, ta zama bakar fata ta farko da ta yi hakan. Ta kammala karatun digiri na farko a fannin fasaha a Turanci da Tarihi. [3]

Kachigwe ta mutu a gidanta da ke Greendale, Harare, a cikin shekarar 2012 daga matsalolin da suka shafi cututtukan zuciya. Jana'izar ta ya samu halartar mataimakin firaministan ƙasar Farfesa Arthur Mutambara da jakadan Malawi a Zimbabwe Dr Richard Mpoya. An binne ta a makabartar Greendale ta Harare. [1]

A wajen jana'izar ta, mataimakin firaministan ƙasar Arthur Mutambara ya miƙa tutar ƙasar Zimbabwe ga mijin Misis Kachingwe don nuna matsayinta na "jarumar yakin kwato 'yanci". [2]

  1. 1 2 Machirori, Fungai (6 August 2012). "Women who've broken ground in Zimbabwe". Her Zimbabwe. Archived from the original on 11 February 2018. Retrieved 10 February 2018.
  2. 1 2 3 Fungai Machirori (11 June 2012). "Heroine Kachingwe buried". The Herald. Retrieved 10 February 2018.
  3. "Liberation war heroine Kachingwe laid to rest". Nehanda Radio. 10 June 2012. Archived from the original on 11 February 2018. Retrieved 10 February 2018.