Sebhat Ephrem
|
| |||||||
2014 - ← Ahmed Haj Ali (en)
1995 - 2013 ← Mesfin Hagos - Filipos Woldeyohannes (en)
1994 - 1995 ← Haile Mehtsun (en) | |||||||
| Rayuwa | |||||||
| Haihuwa | Asmara, 1951 (74/75 shekaru) | ||||||
| ƙasa | Eritrea | ||||||
| Sana'a | |||||||
| Sana'a | ɗan siyasa da Mai kare Haƙƙin kai | ||||||
| Imani | |||||||
| Jam'iyar siyasa |
People's Front for Democracy and Justice (en) | ||||||
Sebhat Ephrem (Tigrinya: Sab ኤፍረም; an haife shi a shekara ta 1951) wani jami'in sojan Eritrea ne kuma ɗan siyasa wanda shi ne Ministan Makamashi da Ma'adinai na Eritrea.[1] Ya kuma kasance tsohon ministan tsaro kuma tsohon kwamandan kungiyar EPLF a lokacin yakin neman ‘yancin kai na Eritrea.
Rayuwar farko
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Sebhat Ephrem a Aksum, Habasha ga iyayen Eritrea daga Asmara.[1] Mahaifinsa ma'aikacin asibiti ne mai ilimin Furotesta kuma Sebhat ya halarci Makarantar Evangelical Lutheran a Asmara, Eritrea. Daga nan ya yi karatun kantin magani a jami'ar Addis Ababa na tsawon shekaru biyu kafin ya shiga ƙungiyar ta EPLF a shekarar 1972.[1]
Aikin soja
[gyara sashe | gyara masomin]Ya yi gaggawar hawa muƙami daga kwamishinan siyasa har ya zama ɗan kwamitin zartarwa a shekarar 1977.[1] Ya zama Janar na EPLA a cikin shekarar 1986 kuma an ba shi matsayin jagoran dabarun nasara a Afabet, Massawa da Dekemhare.[1] Bayan samun 'yanci Sebhat Ephrem ya yi aiki daga watan Yuni 1992 zuwa watan Maris 1994 a matsayin Gwamnan Asmara. Daga watan Maris 1994 zuwa watan Mayu 1995 ya zama Ministan Lafiya.[1] A duka muƙaman biyu ya kawo tsari da sake fasalin waɗannan ofisoshin. Bayan ya bar aikin soja a watan Yunin 1992, ya koma soja a watan Mayun 1995 da muƙamin Janar aka naɗa shi kuma aka tabbatar da shi a matsayin ministan tsaro. An yi imanin cewa a cikin shekarar 1998 shi ne kawai janar mai taurari 4 a cikin sojojin tsaron Eritrea.[1]