Shehu Idris

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Shehu Idris
18. Sarkin Zazzau

8 ga Faburairu, 1975 - 20 Satumba 2020
Muhammadu Aminu (en) Fassara - Ahmed Nuhu Bamalli
Rayuwa
Haihuwa Zariya, 20 ga Faburairu, 1936
ƙasa Najeriya
Mutuwa Kaduna, 20 Satumba 2020
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a Malami
Imani
Addini Musulunci
masarautar Zazzau 09

Shehu Idris (An haife shi a shekarar 1936 ya rasu a shekarar 2020), ya kasance shine Sarkin Zazzau na goma sha takwas 18 a jerin sarakunan Zariya dake Jihar Kaduna,[1] a sarakunan Fulani a karkashin Daular usmanniya ta Musulunci Sokoto Najeriya.[2] Shehu idris shine da na biyar a wajen mahaifiyarsa kuma da na shida a cikin maza a wajen mahaifinsa. Shehu Idiris ya kasance shine mafi tsawon mulki a tarihin masarautar ƙasar Zazzau, ya kwashe tsawon shekaru 45 a sarautar.Ya hau karagar mulki tun a 8 ga watan Fabrairu shekarar alif 1975 biyo bayan rasuwar Sarkin Zazzau na goma sha bakwai Muhammadu Aminu a sanda Idris yake da shekaru 39 a rayuwarsa.[3][4] Mahaifinsa shine Malam Idris Auta, mahaifiyarsa kuma itace Hajiya Aminatu Idris.[5].

Farkon Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Tarihin mai martaba sarkin zazzau Alhaji Shehu Idris ya fara ne daga Ranar 20 ga watan Fabrairu a shekara ta 1936, wanda shine asalin ranar da aka haifawa malam Idiris Autan Sambo da malama Aminatu matarsa ta uku (mahaifan shehu Idris). Bayan sati daya da haihuwarsa an sanya ma yaron suna SHEHU USMAN kaman yadda addini da al’ada suka tanadar. An haifi Idris daga gidan malam Idiris Auta wanda akafi sani da Auta Sambo tare da matarsa Hajiya Aminatu.[6][7]

Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

Shehu ya fara karatu yana ɗan shekara biyar. A wannan shekarun ba’a aika shi makarantar nursery ko firamari ba sai dai an tura shi makarantar islamiyya inda ya koyo karatun Al-Qur’ani kamar yadda addini ya tanadar. Shehu ya kasance dalibi mafi kwazo a lokacin da yake zuwa makarantar allo, saboda baya taba yin fashin ajin safe ko na yamma ba tare da wani dalili mai ƙarfi ba. Ranaku biyar ne ake zuwa makarantar a sati watau daga Asabar zuwa laraba ƙarfe 7:30 zuwa 11:30 da safe, sai kuma 2:30 zuwa 6:00 da yamma.[8] A lokacin da ya kai shekara 11 an sanyashi makarantar zamani a nan garin Zariya  a shekarar 1947. Duk da yana zuwa makarantar boko domin neman ilimin zamani, hakan bai hana shi cigaba da karatunsa na addini ba.[8].

Sarauta[gyara sashe | gyara masomin]

Shehu Idris ya zama Sarki ne sanda Jihar take a matsayin Jihar Arewa ta Tsakiya a shekara ta 1975. A shekarar mai zuwa, Janar Murtala Mohammed lokacin yana Shugaban ƙasa ya canja mata suna zuwa Jihar Kaduna. Bayan an kwashe shekaru goma sha ɗaya, sai Janar Ibrahim Babangida ya raba jihar zuwa gida biyu Katsina da Jihar Kaduna a shekara ta 1987. Inda rabewar ya haifar da natsuwa akan tashin hankalin dake faruwa tsakanin Masarautar Katsina da ta Zazzau a sanda suke jiha ɗaya. Amma duk da wancan rabewar kuma, sai aka sake samo wata sabuwar rabuwa tsakanin mutanen dake rayuwa a kudancin Kaduna da Arewacin Kaduna.[9][10] Idris ya fara karatunsa ne daga samun koyarwa na addini a wurin malamai a Zariya da Kuma cigaba da karatun sa a makarantar Zariya Elementary School.[11] Yana elementary school dafa a shekarar 1947 zuwa shekara ta 1950, Inda a wannan lokacin ya rasa mahaifinsa yana da shekara 12.[11] Idris ya cigaba da karatun alkur’ani da na zamani har yakai ga Zariya Middle School a shekarar 1950 sa'annan ya kammala karatunsa a shekarar 1955.[11] Sannan ya shiga Katsina Training College inda yazama malamin makaranta mai koyarwa.[7]

Wanda wannan rabuwa ta haifar da rashin jituwa da dama. Waɗanda suka shahara sune Rikicin Kafanchan a shekarar 1987, Faɗan Zangon Kataf sau biyu a shekarar 1992, faɗan Shari’a a 2000 da kuma faɗan bayan zaɓen shekara ta 2011 da shekara ta 2012. Lokacin sarautar Shehu Idris, yawancin dukkanin yankunan al'umma dake cikin garin Zazzau waɗanda ba Hausawa ba an basu cin gashin kansu kuma suka zama Masarautun kansu. Wannan yakamata ya baƙanta ma Idris rai. Biyo bayan ƙirƙiran wata sabuwar masarauta a 2001, wasu bangaren Musulmai dake Zazzau suma sun nemi a basu cin gashin kansu. Samun kaiwa shekaru 45 a sarauta ba ƙaramin abu bane, Kuma ya zamo mafi tsawon mulki a tarihin sarautar Zazzau.

A yan' wannan karnin, an sha samun tsige-tsigen sarakunan gargajiya a masarautun Arewacin Najeriya. Sultan Ibrahim Dasuki an tsige shi a 1996, sarkin Gwandu Almustapha Jokolo an tsige shi a 2005 da Kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II shi ma an tsige shi a farkon shekarar 2020. Haka Kuma sarakunan a Muri, Suleja da Agaie. Sai dai Sarkin Zazzau ya kiyaye wa kansa duk wani abunda zai sanya asamu matsala tsakanin shi da wani Shugaba.

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Idris nada shekaru 39 ne a sanda ya zama Sarkin Zazzau a watan Fabrairu na shekara ta 1975. Gabanin hawan sa sarauta ya kasance hakimi Kuma malamin makaranta. Gwamnan Kaduna na wancan lokacin Birgediya Abba Kyari shine ya naɗa Shehu Idris a matsayin Sarkin Zazzau na sha takwas a shekara ta 1975.

Shehu Idris a makarantar sakandiri

Dangi[gyara sashe | gyara masomin]

Shehu shine ɗa na biyar a wajen mahaifiyarsa kuma ɗa na shida a cikin maza a wajen mahaifinsa. Shehu ƙarami ya kasance kyauta ne mai matuƙar rahama daga Allah wanda iyayensa suka yiwa Allah godiya akan samunsa da suka yi.[12] Shehu Idris ya taso ne a gidan yawa saboda mahaifinsa yana da mata har guda huɗu, kuma gidan ya kasance daga sashin mulkin katsinawa a zazzau. Shehu ya samu tarbiyya kai tsaye daga wajen iyayensa malam Idris Autan Sambo da malama Aminatu tare da taimakon sauran iyayensa mata na gida. Malama Suwaibatu, Malama Zainabu, Malama Raliyatu. Kuma dukkanin su sun karkatu ne akan tarbiyya ta addini da kuma al’adu na ƙwarai. Al’ada ne a ƙasar hausa uwa take ɓoye sunan ɗanta na farko ko na biyu saboda alkunya, amma malama Aminatu ta ɓoye gaba ɗaya sunayen yaranta guda biyar inda kowanne ta bashi laƙabi da take kiransa da shi, ya kasance shehu ya samu suna “Na Allah”. Kuma ta kanyi wasa dashi a matsayin yaronta na biyar.[12] Shehu ƙarami ya kasance kyauta ne mai matuƙar rahama daga Allah wanda iyayensa suka yiwa Allah godiya akan samunsa da suka yi.[13]

Mutuwa[gyara sashe | gyara masomin]

A yanzu bayan rasuwar Alhaji Shehu Idris gasar data daɗe a kwance ta tashi tsakanin a wane gida ne Sabon sarki zai fito, Barebari, Mallawa, Sullubawa ne ko kuma daga gidan Shehu Idris Katsinawa. Yarimomi sun daɗe tsawon shekaru 45 suna jiran wannan damar.

Hotuna[gyara sashe | gyara masomin]

Bibilyo[gyara sashe | gyara masomin]

  • Dalhatu, Ibrahim. Alhaji Shehu Idris, the 18th fulani emir of zazzau. Hassan, Musa. ISBN 978-2118-028

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Buhari, N-Govs, others mourn as Emir of Zazzau, Shehu Idris dies at 84". Vanguard News (in Turanci). 2020-09-21. Retrieved 2022-03-17.
  2. Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named breaking
  3. "Zazzau Emirate Council Member shot dead in Kaduna". Premium. Retrieved 10 November 2015.
  4. "I Owe Long Life, Peaceful Coexistence To Almighty Allah – Shehu Idris". Leadership Newspaper. Archived from the original on 9 September 2015. Retrieved 10 November 2015.
  5. https://dailytrust.com/history-beckons-as-emir-of-zazzau-marks-45th-anniversary
  6. "Emir Shehu Idris of Zazzau: Exit of a gentleman peacemaker". www.pressreader.com. Retrieved 21 September 2020.
  7. 7.0 7.1 Marshal, Adamu (14 January 2015). "HH Alhaji Shehi Idris". Kabidonews.com. Archived from the original on 7 May 2016. Retrieved 30 April 2016.
  8. 8.0 8.1 Dalhatu, Ibrahim. Alhaji Shehu Idris,the 18th fulani emir of zazzau. Hassan, Musa. p.p. 60-63 ISBN 978-2118-028
  9. "Zazzau Emirate Council Member shot dead in Kaduna". Premium. Retrieved 10 November 2015.
  10. "I Owe Long Life, Peaceful Coexistence To Almighty Allah – Shehu Idris". Leadership Newspaper. Archived from the original on 9 September 2015. Retrieved 10 November 2015.
  11. 11.0 11.1 11.2 "The Emir of Zazzau, His royal Highness Alh(Dr) Shehu Idris, is dead". NewsWire NGR. Retrieved 21 September 2020.
  12. 12.0 12.1 Dalhatu, Ibrahim. Alhaji Shehu Idris, the 18th fulani emir of zazzau. Hassan, Musa. p.p. 57-59 ISBN 978-2118-028
  13. Dalhatu, Ibrahim. Alhaji Shehu Idris, the 18th fulani emir of zazzau. Hassan, Musa. p.p. 57-59 ISBN 978-2118-028