Yaki A Uganda (1968 1994)
| Iri |
civil war (en) |
|---|---|
Daga shekarar 1986 zuwa 1994, kungiyoyin 'yan tawaye daban-daban sun kaddamar da yakin basasa da gwamnatin shugaba Yoweri Museveni na Uganda. Galibin fadan dai ya faru ne a arewaci da gabashin kasar, duk da cewa yankunan yammaci da tsakiyar kasar ma abin ya shafa. Bangarorin masu tayar da kayar baya sun hada da Uganda People's Democratic Army (UPDA), Uganda People's Army (UPA), Alice Auma's Holy Spirit Movement (HSM), da kuma Joseph Kony (wanda daga baya ya zama Lord's Resistance Army). Wasu ƙananan ƙungiyoyin 'yan tawaye da ƙungiyoyin ɓangarorin manyan ƙungiyoyi sun gudanar da nasu kamfen; 'Yan tawayen sun sha yin arangama da juna. Dukkanin maharan, ciki har da gwamnati, sun kai hari kan fararen hula tare da keta hakin bil'adama. A yayin da ake gwabza fadan da ya hada dubun dubatan dakaru, gwamnatin Uganda ta samu nasarar fatattakar 'yan tawaye a hankali ko kuma ta dakushe mafi yawan bangarorin 'yan tawaye. Ayyukan da aka yi a arewaci da gabas sun haifar da barna mai yawa tare da haddasa asarar rayuka da dama.By 1994, the HSM and UPDA had disintegrated, the UPA had been reduced to small splinter groups, and Joseph Kony and his forces were at least weakened. However, the situation in the entire region drastically shifted in that year, as outside powers intervened and began to fund insurgencies to topple Museveni. In turn, Uganda was drawn into cross-border conflicts in Zaire and Sudan. These developments resulted in a resurgence of insurgent activity in northern Uganda. Several groups which emerged during the 1986–1994 conflict, including Kony's Lord's Resistance Army, continue their insurgencies to the present day.
Asali
[gyara sashe | gyara masomin]Bayan samun 'yancin kai a shekara ta 1962, Uganda ta fada karkashin gwamnatocin kama-karya, ta sha fama da rikicin tattalin arziki, kuma ta fuskanci rikice-rikicen soji da dama. A shekarar 1979, an hambarar da shugaban kasar Uganda Idi Amin a lokacin yakin Uganda-Tanzaniya, sannan kuma tsohon shugaban kasar Milton Obote ya dawo kan mulki.[1] Sassan sojojin Uganda na Amin da ƙungiyoyin adawa da Obote daban-daban sun kaddamar da tawaye, wanda ya haifar da yakin Bush na Uganda mai barna sosai.[2]