Jump to content

Yerima Usman Shettima

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Yerima Usman Shettima
Yerima Usman Shettima a shekarar 2023
Haihuwa (1974-05-28) 28 Mayu 1974 (shekaru 51)
Jihar Kaduna, Najeriya
Matakin ilimi Jami'ar Jihar Legas, Jami'ar Jihar Kaduna
Aiki MD/CEO Shehalfat Properties and Logistics, Dan gwagwarmayar kare hakkin dan adam, Wanda ya kafa Arewa Youths Consultative Forum, Dan jarida.
Uwar gida(s) Halima Shettima da Fatima Shettima
Yara Rahmat Shettima, Raliya Shettima, Muhammad Sani Shettima, Salisu Mujjahid Shettima, Aisha Humaira Shettima, Muhammad Shafiu Shettima, Raliya Ihsan Shettima
Iyaye(s) Alhaji Shafi'u Usman da Hajiya Raliya Muhammad

Yerima Usman Shettima (an haife shi a ranar 28 ga Mayu, 1974) dan asalin Kaduna, Najeriya ne, Dan gwagwarmayar kare hakkin dan adam, Dan jarida, Mawallafi, da kuma mai rajin kare dimokuradiyya. Shi ne Manajan Darakta da Babban Jami'in Kamfanin Shehalfat Properties and Logistics, kuma shi ne wanda ya kafa kuma shugaban kungiyar Arewa Youths Consultative Forum (AYCF).[1]

Rayuwar Farko

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Yerima Usman Shettima a ranar 28 ga Mayu, 1974 a Zariya, Jihar Kaduna, Najeriya. Ya fito daga iyalan Fulani kuma an tashe shi bisa koyarwar addinin Musulunci. Ya fara karatunsa a makarantar Islamiya a Otukpo, Jihar Benue. Daga nan ya ci gaba da karatu a Nico Commercial Secondary School da ke Jihar Cross River. Bayan haka, ya halarci Jami'ar Jihar Legas (LASU), inda ya samu Digiri a fannin Gudanar da Harkokin Jama'a. Ya kuma kammala Digiri na biyu a fannin nazarin rikici, zaman lafiya, da dabarun siyasa a Jami'ar Jihar Kaduna.[2]

Aikin Farko

[gyara sashe | gyara masomin]

Ya fara aikinsa ne a matsayin Shugaban Kamfanin Shehalfat Properties and Logistics Limited a Jihar Kaduna. Ya kasance memba mai tasiri a kungiyar NADECO, kuma shi ne wanda ya kafa Arewa Youths Consultative Forum (AYCF). Daga shekarar 2004 zuwa 2006, Yerima Usman Shettima ya kasance Daraktan Matasa a PRONACO, tare da manyan mutane kamar Wole Soyinka, Anthony Enahoro, da Beko Ransom Kuti. Shi ne daya daga cikin wadanda suka kafa kungiyar Save Nigeria tare da Tunde Bakare.[3]

Ya fara harkar siyasa ne a matsayin Mataimakin Shugaban Jam'iyyar Democratic Party for a People's Federation (DPPF) na Arewa maso Gabas tare da jagorancin Wole Soyinka. A shekarar 2011, ya zama mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Liberal Democratic Party of Nigeria (LDPN). A shekarar 2019, ya tsaya takarar Majalisar Wakilai a Kaduna North. A shekarar 2014, ya zama dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar Young Democratic Party (YDP).[4]

Gwagwarmaya

[gyara sashe | gyara masomin]

Yerima Usman Shettima ya kasance babban dan gwagwarmaya da ya taka rawar gani a yakin kawar da mulkin soja da tabbatar da mulkin dimokuradiyya a Najeriya. Ya sha tsarewa a ofishin DSS da kuma ofisoshin ‘yan sanda saboda gwagwarmayarsa na kare ‘yancin dan adam da adalci. Daga cikin wadanda suka yi gwagwarmaya tare da shi, da dama sun rasa rayukansu, amma shi ya tsira daga cin zarafin sojoji.

Rayuwar Kansa

[gyara sashe | gyara masomin]

Yerima Usman Shettima ya auri mata biyu, Hajiya Halima Shettima da Hajiya Fatima Shettima, kuma yana da yara da yawa.[5]

Kyautuka da Karramawa

[gyara sashe | gyara masomin]
  • Lambar yabo daga Ijaw Youth Development Association.
  • Lambar yabo daga Centre for Resolution and NGO Promoting Peace and Unity.
  • Karramawa a matsayin Jakadan zaman lafiya da yaki da rikici.
  • Jakadan kare hakkin dan adam daga Global Forum for Peace Justice and Human Rights.
  • Shaidar karramawa daga Per ASPERAAD Astra.
  • Jakadan zaman lafiya da yawon bude ido daga Ijaw Monitoring Group (IMG).[6]
  • An nada shi da sarautar Jarman Legas.
  • Ya samu sarautar Omeudo Ndigbo daga Obi Eziokwundigbo na Mushin Land.[7]
  1. "appoint shettima into your cabinet youth groups urge tinubu". Blueprint.ng (in Turanci). 2023-08-28. Retrieved 2023-08-28.
  2. "appoint yerima shettima minister from kaduna Niger delta Youths tell tinubu". Vanguard.ng (in Turanci). 2023-08-29. Retrieved 2023-08-29.
  3. "alhaji yerima shettima president arewa youth consultative Forum aycf 2023 clamouring for Southern president greedy selfish". sunnewsonline.com (in Turanci). 2022-03-12. Retrieved 2022-03-12.
  4. "arewa Youths demand inclusion of yerima shettima in tinubu cabinet". Vanguard.ng (in Turanci). 2023-09-01. Retrieved 2023-09-01.
  5. "why marriages crash very fast fati ladan". blueprint.ng (in Turanci). 2023-12-22. Retrieved 2023-12-22.
  6. "NGo unveil nominees for global peace Humanitarian awards 2023". leadership.ng (in Turanci). 2023-08-10. Retrieved 2023-08-10.[permanent dead link]
  7. "emefiele arewa leader in South wife detained by dss relatives protest". Dailytrust (in Turanci). 2023-07-18. Retrieved 2023-07-18.