Tukur Yusuf Buratai
|
| |||||
13 ga Yuli, 2015 - 26 ga Janairu, 2021 ← Kenneth Minimah - Ibrahim Attahiru →
Mayu 2014 - ga Yuli, 2015 | |||||
| Rayuwa | |||||
| Haihuwa | Biu, 24 Nuwamba, 1960 (65 shekaru) | ||||
| ƙasa | Najeriya | ||||
| Harshen uwa | Babur | ||||
| Karatu | |||||
| Makaranta |
Jami'ar Maiduguri Jami'ar Tsaron Nijeriya | ||||
| Harsuna |
Turanci Babur Kanuri Pidgin na Najeriya | ||||
| Sana'a | |||||
| Sana'a | soja | ||||
| Aikin soja | |||||
| Digiri |
lieutenant general (en) | ||||
| Ya faɗaci | Rikicin Boko Haram | ||||
Tukur Yusuf Buratai
Tukur Yusuf Buratai (Taimako·bayani) Laftanar Janar din soja ne a Najeriya kuma tsohun shugaban sojojin kasan Najeriya wanda Muhammadu Buhari ya nada shi tun a 2015.
An haife shi a garin Buratai dake
karamar hukumar Biu ta jihar Borno, a ranar 24
ga watan Nuwamba a shekarar 1960. Don haka,
Buratai ɗan asalin jihar Borno ne dake arewa
maso gabashin Najeriya.

Laftana Janar TY Buratai shi ne hafsan Sojoji na ashirin da shida 26 a tarayyar Najeriya, wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya naɗa a ranar 13 ga watan Juni na shekarar 2015.
Burtai ya yi karatun Furamari a garinsu buratai, daga nan ne ya zarce zuwa Kwalejin Malaman Gwamnati dake garin Potiskum a jihar Yobe. A watan Junairu na shekarar 1981, Buratai ya halarci Nigerian Defence Academy dake Kaduna a matsayin ɗaya daga cikin membobi a shirin nan na ‘29 Regular Combatant Course (29R)’. Haka zalika, Burtai ya samu takardar shaidar kammala Jami’a, wato Digiri a fannin History daga Jami’ar Maiduguri. Kuma yana da Digiri a fannin Philosophy daga Jami’ar Bangladesh University of Professions dake garin Dhaka.
Kafin naɗinsa a matsayin hafsan Soji, Buratai shi ke jagorantar rundunar tsaro ta hadin–gwiwa wacce ke da hedikwata a birnin Ndjamena na kasar Chadi. Kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da kuma Benin ne suka kafa rundunar domin yaki da ’yan ta’addan da ke yankinsu.
A baya dai, Janar Buratai ya yi aiki a matsayin Kwamandan runduna ta Biyu ta sojin Najeriya dake birnin Fatakwal na jihar Rivers, sannan ya taba zama Kwamandan makarantar horas da sojin kasa dake Jaji, a jihar Kaduna.
Tarihin sa da karatun sa
[gyara sashe | gyara masomin]
Janar Buratai an haifeshi a garin Buratai, karamar hukumar Biu ta jahar Borno. Mahaifinsa Yusuf Buratai ma tsohon soja ne na Royal West African Frontier Force da kuma Yakin duniya na biyu inda yayi yaki a kasar Burma. Buratai yayi karatunsa na firamare a garin Buratai daga nan kuma ya samu takarar shiga makarantar horar da malamai ta garin Potiskum dake jahar Yobe, inda ya kammala da kyakkyawab sakamako.
Shiga Aikin Soja
[gyara sashe | gyara masomin]
A watana janairu na 1981, Buaratai ya shiga makarantar horar da sojoji dake garin Kaduna. Sakamakon gwaggwabar nasarar da ya samu ta kammalawa ne sai ya samu matsayin Laftanar na biyu a ranar 17 ga Disamba na 1983 a cikin Kuratan sojojin Najeriya. Buratai yayi digiri a fannin ilimin tarihi a jami'ar Maiduguri da kuma wani digirin a fannin falsafa daga jami'ar kwararru ta kasar Bangalidash wato Bangladesh University of Professionals, Dhaka. Ya kuma yi karatu a makaranatr National Defence college, Mirpur, duka a kasar ta Bangalidash.
Ya shiga bataliyar matasan sojoji ta 26 a garin Elele dake Fatakwal, sai kuma mai nazari na harkar soja cikin rundunar sojoji ta majalisar dinkin duniya a kasar Angola, daga baya kuma sai yakoma bataliyar sojojin tsaro a 26 a Lagos wato Lagosa Garroson command Camp. Laftanar Janar Buratai kuma ya rike mukamin mai tafiyarwa na gidan yankin jaha a Abuja; wato 82 Motoruzed Batalion; sai 81 Balation, Bakasi Penninsular; Army Headquaters Garrison, Abuja kafin daga baya kuma sai yazama daraktan ma'aikata a kwalejin horon mayan jami'an soja dake Jaji.


Ya kuma rike makamai kamar haka; AHQ Army Policy and Plans, Abuja; Mataimakin Shugaban tsare tsare na al'amuran gudabarwa, HQ Infantry Centre Jaji. Yadai rike mukamai da dama a bangarori daban daban.
Manyan Ayyuka a Matsayin Shugaban Rundunar Sojin Kasa
[gyara sashe | gyara masomin]Bayan nadin sa a matsayin Shugaban Rundunar Sojin Kasa, Tukur Yusuf Buratai ya jagoranci ayyukan soji da dama da suka shafi yaki da 'yan ta'addan Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya. A cikin watanni na farko da fara aiki, dakarun Najeriya sun sake karɓar iko a yankuna irin su Gamboru Ngala, wanda a baya 'yan ta'adda suka mamaye.[1][2][3][4][5][6]
A ranar 25 ga Yuli 2017, Buratai ya amince da karin girma na musamman ga sojoji 6,199 da suka shiga ayyukan yakar 'yan ta'adda.[7]
Buratai ya kuma ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka da suka shafi ci gaban ababen more rayuwa da walwalar sojoji a Najeriya. Wannan ya haɗa da kafa gonakin soja da kiwo (Nigerian Army Farms and Ranches), gine-ginen gidaje a wurare kamar Jaji da sansanin Khobe (Jihar Filato), da kuma gyaran ruwa da gidan baƙi.[8][9]
A zamaninsa, an kafa cibiyoyi da dama da kuma shirye-shirye na musamman, ciki har da:
- Cibiyar Fasaha da Nazarin Muhalli ta Sojojin Kasa, Biu
- Makarantar Sakandare ta Command, Kebbi
- Ginin matatar jiragen sama ta soji, Jaji
- Rundunar Yaƙin Cyberwar ta Sojojin Kasa
- Kamfanin Kera Motocin Sojoji na Najeriya
- Kwalejin Yaƙi na Sojojin Kasa (Army War College Nigeria)
- Gidan Tarihi na Yaƙin Ta'addanci da Yakkin Yankewa
- Asibitin Matayen Jami’an Sojojin Kasa
- Gidajen soja (misali: Tinapa da Otukpo Post Housing Developments)
- Kamfanin Kasuwancin Noma na Sojojin Kasa
- Rundunonin Special Forces da kuma na Babura
- Motar sintiri mai kariya daga fashewa (MRAP) da sauran na'urorin gida
- Kafa Division na 6 da 8
- Cibiyar Koyon Harsunan Najeriya
[10] [11] [12] [13] [14] [15] [16] [17] [18] [19] [20] [21] [22] [23] [24] [25]
Wallafe-wallafe
[gyara sashe | gyara masomin]Tukur Yusuf Buratai yana da alaƙa da wasu wallafe-wallafe da suka haɗa da batutuwa kan jagoranci, gogewar soja, da kuma labaran ƙirƙira:
- The Legend of Buratai (2020) – littafi ne na yara da ke ƙunshe da labarin ƙirƙira wanda aka samo daga tarihin aikinsa.[26]
- Thought and Principles on Leadership (2022) – littafi ne da ke bayyana kimar jagoranci da ƙa'idodin rayuwa na mutum.[27]
- Nigeria’s War on Terror – wallafa ce da ke tattauna dabarun yaƙin Najeriya da ta'addanci da tsare-tsaren tsaro.[28]
- Makintakururi: The Disaster That Never Was – cikakkun bayanai ba su samuwa a yanzu.
- In the Mind of the General – cikakkun bayanai ba su samuwa a yanzu.
Lambobin Yabo
[gyara sashe | gyara masomin]Lambobin yabo da karramawa da Laftanar Janar Buratai ya samu sun haɗa da:
- Tauraron Sabis na Soji (FSS)
- Tauraron Sabis na Kwarewa (MSS)
- Tauraron Sabis na Girmamawa (DSS)
- Tauraron Sabis na Babban Mataki (GSS)
- Kammala Kwasa-Kwase na Ma’aikata da Digga (psc(+))
- Lambar Girmamawa ta Jagoranci a Filin Daga
- Lambar Tallafin Horarwa
- Lambar MDD don Aikin Tantancewa a Angola (Angolan Verification Medal II)
- 2022 – Kwamandan Jihar Tarayyar Najeriya (CFR)[29]
Ranakun da ya samu Karin Girma
[gyara sashe | gyara masomin]Ranakun da aka ba Buratai karin girma sune[30]
| Shekara | Tambarin Girma | Matsayi |
|---|---|---|
| Disamba 1983 | Laftanar na biyu (An ba shi mukami) | |
| 1985 | Laftana | |
| 1989 | Kyaftin | |
| 1994 | Mejo | |
| 1998 | Laftanar Kanar | |
| 2004 | Kanar | |
| 2009 | Brijadiya Janar | |
| 2012 | Mejo Janar | |
| Agusta 2015 | Laftanar Janar[31] |
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "Nigerian president replaces military top brass". aljazeera.com (in Turanci). 2015-07-14. Retrieved 2015-07-14.
- ↑ "Nigeria military recaptures border town from Boko Haram". dailytimesng.com (in Turanci). 2020-09-25. Retrieved 2020-09-25.
- ↑ "Nigerian troops cross border after Boko Haram clashes". bbc.com (in Turanci). 2016-04-25. Retrieved 2016-04-25.
- ↑ "Nigerian army blockades Boko Haram base". aljazeera.com (in Turanci). 2013-05-20. Retrieved 2013-05-20.
- ↑ "Wasu sojojin Nijeriya sun yi Allah wadai da Buratai". bbc.com (in Turanci). 2020-05-20. Retrieved 2020-05-20.
- ↑ "Nigeria mass abduction seen as copycat attack". wsj.com (in Turanci). 2022-02-22. Retrieved 2022-02-22.
- ↑ "Operation Lafiya Dole: Buratai grants special promotion to 6,199 soldiers". dailytrust.com (in Turanci). 2017-07-25. Retrieved 2017-07-25.
- ↑ "Buratai inspects multiple projects in Jos Cantonment". guardian.ng (in Turanci). 2020-09-25. Retrieved 2020-09-25.
- ↑ "Buratai says Nigerian Army Farm and Ranches Limited will reduce unemployment, insecurity". guardian.ng (in Turanci). 2020-12-29. Retrieved 2020-12-29.
- ↑ "Nigerian Army commissions smart factory building and accommodation for its personnel". thewhistler.ng (in Turanci). 2018-08-25. Retrieved 2018-08-25.
- ↑ "Nigerian army creates new division in South-South". pmnewsnigeria.com (in Turanci). 2016-01-14. Retrieved 2016-01-14.
- ↑ "Buratai launches banking scheme for army in Taraba". dailytrust.com (in Turanci). 2021-01-28. Retrieved 2021-01-28.
- ↑ "Buratai visits troops of Operation Lafiya Dole". guardian.ng (in Turanci). 2019-11-29. Retrieved 2019-11-29.
- ↑ "Baba Buhari emerges best participant at Army War College". dailypost.ng (in Turanci). 2020-11-27. Retrieved 2020-11-27.
- ↑ "Nigerian Army formalises collaboration with firm on food security". nannews.ng (in Turanci). 2025-01-07. Retrieved 2025-01-07.
- ↑ "Nigerian Army Vehicles Manufacturing Company". theeagleonline.com.ng (in Turanci). 2020-02-15. Retrieved 2020-02-15.
- ↑ "Buratai still focused on victory over Boko Haram". thecable.ng (in Turanci). 2019-04-25. Retrieved 2019-04-25.
- ↑ "Army budgets 3.350 billion naira for new aviation unit, drone command centre". dailytrust.com (in Turanci). 2020-03-22. Retrieved 2020-03-22.
- ↑ "Nigerian Army's Cyber Warfare Command begins operation". vanguardngr.com (in Turanci). 2018-08-12. Retrieved 2018-08-12.
- ↑ "Insurgency: Army unveils Nigerian-made anti-ambush protected vehicles". businessday.ng (in Turanci). 2016-04-25. Retrieved 2016-04-25.
- ↑ "Buratai left legacy of service transformation in the army – Analyst". vanguardngr.com (in Turanci). 2025-06-20. Retrieved 2025-06-20.
- ↑ "Why Army established farms, ranches – Major General CG Musa". dailytrust.com (in Turanci). 2019-06-15. Retrieved 2019-06-15.
- ↑ "TY Buratai donates 40 books to encourage reading culture among school children". thesun.ng (in Turanci). 2021-04-25. Retrieved 2021-04-25.
- ↑ "Why 6 Division was created in Niger Delta – GOC". punchng.com (in Turanci). 2019-05-20. Retrieved 2019-05-20.
- ↑ "Nigerian Army commissions smart factory building and accommodation for its personnel". thewhistler.ng (in Turanci). 2020-04-25. Retrieved 2020-04-25.
- ↑ "The Legend of Buratai: The children's book and animation that reveals Nigeria's former army chief as the lion killer". sunrise.ng (in Turanci). 2022-01-15. Retrieved 2022-01-15.
- ↑ "Book Review: Principles for greatness from the life of General Tukur Buratai for youths". guardian.ng (in Turanci). 2022-04-25. Retrieved 2022-04-25.
- ↑ "A blueprint for tomorrow's leaders: How General Buratai's life lessons are guiding Nigerian youth to greatness". thisdaylive.com (in Turanci). 2025-04-01. Retrieved 2025-04-01.
- ↑ "FULL LIST: 2022 National Honours Award Recipients The Nation Newspaper". The Nation. 2022-10-09. Retrieved 2022-10-26.
- ↑ Cite error: Invalid
<ref>tag; no text was provided for refs namedNA - ↑ Agba, George. "As Service Chiefs Get Promotion: PMB Gives Marching Orders On Boko Haram". Leadership Nigeria. Archived from the original on 20 August 2015. Retrieved 14 August 2015.