Jump to content

Zaɓen Majalisar Mazabar Aljeriya 1962

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentZaɓen Majalisar Mazabar Aljeriya 1962
Iri Algerian legislative election (en) Fassara
Kwanan watan 20 Satumba 1962
Ƙasa Aljeriya

Creating Zaɓen Majalisar Mazabar Aljeriya 1962 An gudanar da zaben 'yan majalisar dokoki a kasar Aljeriya a ranar 20 ga watan Satumban shekarar 1962, zaben 'yan majalisar dokoki na farko tun bayan samun 'yancin kai a watan Yuli. An gudanar da zaben ne tare da kuri'ar raba gardama da ta tabbatar da iko da tsawon wa'adin majalisar.[1]


Majalisar ta kasance tana da wa'adin shekara guda don tsara kundin tsarin mulki da kuma fitar da shi. An sanya jerin sunayen ‘yan takara guda 196 na ‘yan takarar jam’iyyar National Liberation Front ga masu kada kuri’a don amincewa, 180 daga cikinsu Larabawa ne, 16 daga cikinsu kuma ‘yan asalin Turai ne. An bayar da rahoton kashi 99.6% sun kada kuri’ar amincewa, tare da fitowar kashi 84%.[2]


An amince da kundin tsarin mulkin ne a wata kuri’ar raba gardama a watan Satumba na shekarar 1963, kuma an kara wa’adin Majalisar da shekara guda kamar yadda doka ta 77 ta tanada. Sai dai shugaba Ahmed Ben Bella ya dakatad da ayyukan majalisar tare da samun cikakken iko a ranar 3 ga Oktoban 1963.[3]

  1. The National People's Assembly http://www.algeria-id.org/natpolins/the_national_peoples_assembly.php Archived 2011-07-24 at the Wayback Machine
  2. https://en.wikipedia.org/wiki/Dieter_Nohlen
  3. Algeria, State Institutionshttp://www.algeria-id.org/natpolins/the_national_peoples_assembly.php