Zaben gwamna na Jihar Kaduna na 2011
| Iri |
gubernatorial election (en) |
|---|---|
| Kwanan watan | 28 ga Afirilu, 2011 |
| Ƙasa | Najeriya |
| Applies to jurisdiction (en) | Jihar Kaduna |
A ranar 28 ga Afrilu, 2011 ne aka gudanar da zaben gwamnan jihar Kaduna a shekarar 2011,[1] bayan da aka shafe kwanaki biyu ana yi saboda matsalar tsaro.[2] A cikin sama da jam’iyyun siyasa biyar da suka fafata, biyu ne kacal, PDP da sabuwar jam’iyyar CPC. Dan takarar jam’iyyar PDP kuma gwamna mai ci, Patrick Ibrahim Yakowa, ya doke Haruna Saeed na CPC da wasu 12, inda ya samu kashi 52.34% na yawan kuri’un da aka kada.[3]
Patrick Ibrahim Yakowa ne ya lashe zaben fidda gwani na gwamna a jam’iyyar PDP. Ya rike Mukhtar Ramalan Yero a matsayin abokin takararsa.[4]
Sakamako
[gyara sashe | gyara masomin]‘Yan takara 14 ne suka yi rajista da hukumar zabe mai zaman kanta domin su fafata a zaben. Dan takarar PDP ya samu da kuri’u 1,334,319 da ke wakiltar kashi 52.36% na kuri’un da aka kada, sai dan takarar jam’iyyar CPC wanda ya samu kuri’u 1,133,564 da ke wakiltar kashi 44.46% na yawan kuri’un da aka kada. ANPP ta samu kuri'u 33,142, PRP 21,200, sai ACN 20,094.[5]
Bayan haka
[gyara sashe | gyara masomin]Rikici ya barke bayan zaben kananan hukumomi 18 cikin 23 da ke fadin jihar, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi, inda adadin wadanda suka mutu ya kai 401 zuwa 957, kamar yadda kwamitin bincike na shari’a ya tattara.[6]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ Ojo, Jide. "Nigeria after the 2011 General Elections". ACE. Retrieved March 3, 2021.
- ↑ "Governorship elections: uneven turn-out in Kaduna". IWPR Nigeria. April 29, 2011. Retrieved March 3, 2021
- ↑ "National Election Results | 26 April 2011 State Governorship Elections in Nigeria". African Elections Database. Retrieved March 2, 2021
- ↑ Azikiwe, Ifeoha (2013). Nigeria: Echoes of a Century: Volume Two 1999-2014. p. 160. ISBN 9781481729291. Retrieved May 27, 2021.
- ↑ Adi, Femi (April 29, 2011). "Yakowa wins Kaduna Gov. Election with 1,334,319 votes". Kaduna: PM News. Retrieved March 2, 2021.
- ↑ "Nigeria 2015 Elections Scenarios and Recommendations: Kaduna State". Fund for Peace. January 15, 2015. Retrieved March 4, 2021