Jump to content

Zainab Ahmed

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Zainab Ahmed
Ministan Albarkatun kasa

21 ga Augusta, 2019 - 29 Mayu 2023
Ministan Albarkatun kasa

14 Satumba 2018 - 21 ga Augusta, 2019
Kemi Adeosun
Minister of State for Budget and National Planning (en) Fassara

11 Nuwamba, 2015 - 19 Satumba 2018
Rayuwa
Haihuwa Jihar Kaduna, 16 ga Yuni, 1960 (64 shekaru)
ƙasa Najeriya
Mazauni Jahar Kaduna
Abuja
Harshen uwa Hausa
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Jami'ar Olabisi Onabanjo
Queen Amina College, Kaduna (en) Fassara
Matakin karatu Digiri a kimiyya
MBA (mul) Fassara
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da accountant (en) Fassara
Wurin aiki Jahar Kaduna da Abuja
Employers Jihar Kaduna
NITEL
gwmanatin najeriya
Mamba Association of National Accountants of Nigeria (en) Fassara
Nigerian Institute of Management (en) Fassara
Imani
Jam'iyar siyasa All Progressives Congress
Zainab Ahmed tare da Adebola Williams - Dandalin Tattalin Arzikin Duniya 2023

Zainab Shamsuna Ahmed lafazin magana CON (an haife ta a ranar 16 ga watan Yuni, shekara ta alif dubu daya da ɗari tara da sittin 1960).[1][2] Ta kasance accountant din Najeriya ne, wacce ta yi ministan kudi, kasafin kuɗi da tsare-tsare na ƙasa tun daga shekarar 2019 zuwa shekarar 2023. Ta taba rike mukamin ministar kudi daga shekarar 2018 zuwa shekarar 2019.[3][4] A lokacin shekarar 2019, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kawo ma’aikatun biyu a karkashinta a matsayin ministar tattalin arziki.[ana buƙatar hujja][5][6]

Accountant ce a sana'an tayi digirin farko a fannin lissafi a ABU Zaria sannan kuma ta yi digiri na biyu a fannin kasuwanci (MBA), Ahmed Zainab an nada ta a matsayin ministan kudi bayan murabus din tsohuwar ministar kudi Kemi Adeosun a ranar 14 ga watan Satumba, shekarar 2018. A shekarar 2015 ne shugaba Buhari ya nada ta a matsayin karamar ministar kasafi da tsare-tsare ta kasa.[7]

Rayuwar farko da ilimi

[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Ahmed Zainab a jihar Kaduna.[8] Ta yi karatun sakandare a Kwalejin Queen Amina da ke Kaduna, sannan ta ci gaba da karatun A'Level a Zariya. Ta samu digiri na farko a fannin Accounting a Jami’ar Ahmadu Bello a shekarar 1981, inda daga nan ta wuce Jami’ar Olabisi Onabanjo don yin MBA.[9]

Ahmed Zainab ta samu MBA a watan Agusta shekarar 2004 daga Jami'ar Jihar Ogun, Ago Iwoye; yayin da ta samu BSc Accounting (1981) daga Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya; IJMB 'A' Levels (1979) daga SBS/ABU Zaria; da WASC 'O' Level a shekarar (1977) daga Queen Amina College Kaduna.[10][11][12]

Aikin Siyasa

[gyara sashe | gyara masomin]

Ahmed Zainab ita ce ministan kudi, kasafin kudi da tsare-tsare na kasa na Tarayyar Najeriya. Aikin da ya sa ta zama minista mafi tasiri a ƙasar. A wannan matsayi, tana neman bunkasa kudaden shiga na gwamnati, tare da shirye-shiryen kara yawan harajin da aka kara da ita tare da tauye bashin jama'a wanda a yanzu an kiyasta fiye da dala biliyan 80.[13] Ahmed Zainab ta kasance tsohuwar sakataren zartarwa na kasa kuma coordinator kungiyar fayyace masana'antu ta Najeriya (NEITI). Ta kuma kasance memba a kwamitin NEITI guda biyu na ƙarshe, wanda tayi aiki a NEITI da na duniya EITI.[14]

Bayan kammala karatunta, Ahmed Zainab ta samu aiki a shekarar 1982 a matsayin Accountant II a babban asusu na ma’aikatar kudi ta jihar Kaduna, sannan aka kara mata girma zuwa Accountant I a watan Maris shekarar 1984, amma a shekarar 1985 ta yi murabus ta koma NITEL. Tun da farko ta yi hidimar matasa ta kasa a jihar Kaduna a shekarar 1981 zuwa shekarar 1982 inda aka tura ta aikin farko zuwa Messrs. Egunjobi Suleiman & Co. Chartered Accountants, kuma ta yi aiki a matsayin mai horas da Audit.[15]

Ahmed Zainab ta yi wa al’ummar Najeriya aiki a manyan mukamai daban-daban, ciki har da matsayin manajan darakta na kamfanin saka jari na jihar Kaduna, da kuma babban jami’ar kudi na kamfanin sadarwa ta wayar salula ta Najeriya.[16] An sake nada Zainab kuma aka rantsar da ita a matsayin ministar kudi a ranar 21 ga watan Agusta, shekarar 2019 daga shugaban kasa.[17][18]

Sauran ayyukan

[gyara sashe | gyara masomin]
  • Africa Development Bank (AfDB), tsohon memba na kwamitin gwamnoni (tun 2018)[19]
  • Bankin ECOWAS don Zuba Jari da Ci Gaba (EBID), Tsohon Mamba na Hukumar Gwamnoni (tun a shekarar 2018)
  • Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF), tsohon memba na kwamitin gwamnoni (tun a shekarar 2018)
  • Islamic Development Bank, Tsohon Shugaban Hukumar Gwamnoni (tun a shekarar 2018)
  • world Bank, Tsohon Jami'in Hukumar Gwamnoni (tun a shekarar 2018)

A watan Oktoban shekarar 2022, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba ta lambar girma ta kasa ta Najeriya mai suna Command of the Order of the Niger (CON).

  1. "'Minister's approval of TAT rule at variance with enabling Act'". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2021-10-14. Retrieved 2022-02-22.
  2. Ayitogo, Nasir (21 August 2019). "Buhari assigns portfolios to new ministers". Retrieved 2 September 2019.
  3. "The CVs of Buhari's ministers at a glance". PM News. Retrieved 12 November 2015.
  4. "Nigeria is the hub of stolen cars – Finance Minister, Ahmed Zainab". Naijalitz. 13 August 2021. Retrieved 13 August 2021.
  5. Oladeinde Olawoyin (September 17, 2018). "Zainab Ahmed: The official overseeing Nigeria's finance ministry". Premium Times (in Turanci). Archived from the original on Sep 17, 2018. Retrieved 9 August 2023.
  6. "Zainab Ahmed". World Bank Live (in Turanci). Retrieved 2024-01-22.
  7. "Buhari accepts Adeosun resignation, names Zainab Ahmed as replacement". Cable. 14 September 2018. Retrieved 14 September 2018.
  8. Press, Fellow (17 September 2018). "Finance Minister Zainab Ahmed's profile – Fellow Press". Fellow Press. Archived from the original on 17 September 2018. Retrieved 17 September 2018.
  9. "The CVs Of Buhari's Ministers At A Glance". PM News. Retrieved 14 October 2017.
  10. "Zainab Ahmed: The official overseeing Nigeria's finance ministry". www.premiumtimesng.com. Retrieved 2023-09-09.
  11. "NBET". nbet.com.ng. Retrieved 2024-01-22.
  12. "Zainab Shamsuna Ahmed". EITI (in Turanci). Retrieved 2024-01-22.
  13. "Zainab Ahmed". World Bank Live (in Turanci). 2019-10-01. Retrieved 2021-04-24.
  14. AfricaNews (21 August 2019). "Nigeria's new cabinet inaugurated, president remains Petroleum minister". Africanews. Retrieved 2 September 2019.
  15. "Zainab Ahmed". live.worldbank.org (in Turanci). 2022-01-13. Retrieved 2023-09-20.
  16. TVCN (2018-09-24). "Zainab Ahmed fit for office of finance minister – GOGAN - Trending News" (in Turanci). Retrieved 2023-09-09.
  17. "Fashola gets Works as Ngige, Amaechi, Lai retain portfolios". The Nation Newspaper. 22 August 2019. Retrieved 24 August 2019.
  18. "100Women | Avance Media | Zainab Shamsuna Ahmed" (in Turanci). Retrieved 2024-01-22.
  19. 2019 Annual Report African Development Bank (AfDB).

Samfuri:Finance Ministers of Nigeria