Zainab Ahmed
![]() | |||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|
![]() | |||||||
21 ga Augusta, 2019 - 29 Mayu 2023
14 Satumba 2018 - 21 ga Augusta, 2019 ← Kemi Adeosun
11 Nuwamba, 2015 - 19 Satumba 2018 | |||||||
Rayuwa | |||||||
Haihuwa | Jihar Kaduna, 16 ga Yuni, 1960 (64 shekaru) | ||||||
ƙasa | Najeriya | ||||||
Mazauni |
Jahar Kaduna Abuja | ||||||
Harshen uwa | Hausa | ||||||
Karatu | |||||||
Makaranta |
Jami'ar Ahmadu Bello Jami'ar Olabisi Onabanjo Queen Amina College, Kaduna (en) ![]() | ||||||
Matakin karatu |
Digiri a kimiyya MBA (mul) ![]() | ||||||
Harsuna |
Turanci Pidgin na Najeriya | ||||||
Sana'a | |||||||
Sana'a |
ɗan siyasa da accountant (en) ![]() | ||||||
Mahalarcin
| |||||||
Wurin aiki | Jahar Kaduna da Abuja | ||||||
Employers |
Jihar Kaduna NITEL gwmanatin najeriya | ||||||
Mamba |
Association of National Accountants of Nigeria (en) ![]() Nigerian Institute of Management (en) ![]() | ||||||
Imani | |||||||
Jam'iyar siyasa | All Progressives Congress |


Zainab Shamsuna Ahmed lafazin magana CON (an haife ta a ranar 16 ga watan Yuni, shekara ta alif dubu daya da ɗari tara da sittin 1960).[1][2] Ta kasance accountant din Najeriya ne, wacce ta yi ministan kudi, kasafin kuɗi da tsare-tsare na ƙasa tun daga shekarar 2019 zuwa shekarar 2023. Ta taba rike mukamin ministar kudi daga shekarar 2018 zuwa shekarar 2019.[3][4] A lokacin shekarar 2019, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kawo ma’aikatun biyu a karkashinta a matsayin ministar tattalin arziki.[ana buƙatar hujja][5][6]
Accountant ce a sana'an tayi digirin farko a fannin lissafi a ABU Zaria sannan kuma ta yi digiri na biyu a fannin kasuwanci (MBA), Ahmed Zainab an nada ta a matsayin ministan kudi bayan murabus din tsohuwar ministar kudi Kemi Adeosun a ranar 14 ga watan Satumba, shekarar 2018. A shekarar 2015 ne shugaba Buhari ya nada ta a matsayin karamar ministar kasafi da tsare-tsare ta kasa.[7]
Rayuwar farko da ilimi
[gyara sashe | gyara masomin]An haifi Ahmed Zainab a jihar Kaduna.[8] Ta yi karatun sakandare a Kwalejin Queen Amina da ke Kaduna, sannan ta ci gaba da karatun A'Level a Zariya. Ta samu digiri na farko a fannin Accounting a Jami’ar Ahmadu Bello a shekarar 1981, inda daga nan ta wuce Jami’ar Olabisi Onabanjo don yin MBA.[9]
Ahmed Zainab ta samu MBA a watan Agusta shekarar 2004 daga Jami'ar Jihar Ogun, Ago Iwoye; yayin da ta samu BSc Accounting (1981) daga Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya; IJMB 'A' Levels (1979) daga SBS/ABU Zaria; da WASC 'O' Level a shekarar (1977) daga Queen Amina College Kaduna.[10][11][12]
Aikin Siyasa
[gyara sashe | gyara masomin]Ahmed Zainab ita ce ministan kudi, kasafin kudi da tsare-tsare na kasa na Tarayyar Najeriya. Aikin da ya sa ta zama minista mafi tasiri a ƙasar. A wannan matsayi, tana neman bunkasa kudaden shiga na gwamnati, tare da shirye-shiryen kara yawan harajin da aka kara da ita tare da tauye bashin jama'a wanda a yanzu an kiyasta fiye da dala biliyan 80.[13] Ahmed Zainab ta kasance tsohuwar sakataren zartarwa na kasa kuma coordinator kungiyar fayyace masana'antu ta Najeriya (NEITI). Ta kuma kasance memba a kwamitin NEITI guda biyu na ƙarshe, wanda tayi aiki a NEITI da na duniya EITI.[14]
Bayan kammala karatunta, Ahmed Zainab ta samu aiki a shekarar 1982 a matsayin Accountant II a babban asusu na ma’aikatar kudi ta jihar Kaduna, sannan aka kara mata girma zuwa Accountant I a watan Maris shekarar 1984, amma a shekarar 1985 ta yi murabus ta koma NITEL. Tun da farko ta yi hidimar matasa ta kasa a jihar Kaduna a shekarar 1981 zuwa shekarar 1982 inda aka tura ta aikin farko zuwa Messrs. Egunjobi Suleiman & Co. Chartered Accountants, kuma ta yi aiki a matsayin mai horas da Audit.[15]
Ahmed Zainab ta yi wa al’ummar Najeriya aiki a manyan mukamai daban-daban, ciki har da matsayin manajan darakta na kamfanin saka jari na jihar Kaduna, da kuma babban jami’ar kudi na kamfanin sadarwa ta wayar salula ta Najeriya.[16] An sake nada Zainab kuma aka rantsar da ita a matsayin ministar kudi a ranar 21 ga watan Agusta, shekarar 2019 daga shugaban kasa.[17][18]
Sauran ayyukan
[gyara sashe | gyara masomin]- Africa Development Bank (AfDB), tsohon memba na kwamitin gwamnoni (tun 2018)[19]
- Bankin ECOWAS don Zuba Jari da Ci Gaba (EBID), Tsohon Mamba na Hukumar Gwamnoni (tun a shekarar 2018)
- Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF), tsohon memba na kwamitin gwamnoni (tun a shekarar 2018)
- Islamic Development Bank, Tsohon Shugaban Hukumar Gwamnoni (tun a shekarar 2018)
- world Bank, Tsohon Jami'in Hukumar Gwamnoni (tun a shekarar 2018)
Kyauta
[gyara sashe | gyara masomin]A watan Oktoban shekarar 2022, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba ta lambar girma ta kasa ta Najeriya mai suna Command of the Order of the Niger (CON).
Duba kuma
[gyara sashe | gyara masomin]Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "'Minister's approval of TAT rule at variance with enabling Act'". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2021-10-14. Retrieved 2022-02-22.
- ↑ Ayitogo, Nasir (21 August 2019). "Buhari assigns portfolios to new ministers". Retrieved 2 September 2019.
- ↑ "The CVs of Buhari's ministers at a glance". PM News. Retrieved 12 November 2015.
- ↑ "Nigeria is the hub of stolen cars – Finance Minister, Ahmed Zainab". Naijalitz. 13 August 2021. Retrieved 13 August 2021.
- ↑ "Zainab Ahmed". World Bank Live (in Turanci). Retrieved 2024-01-22.
- ↑ "Buhari accepts Adeosun resignation, names Zainab Ahmed as replacement". Cable. 14 September 2018. Retrieved 14 September 2018.
- ↑ Press, Fellow (17 September 2018). "Finance Minister Zainab Ahmed's profile – Fellow Press". Fellow Press. Archived from the original on 17 September 2018. Retrieved 17 September 2018.
- ↑ "The CVs Of Buhari's Ministers At A Glance". PM News. Retrieved 14 October 2017.
- ↑ "Zainab Ahmed: The official overseeing Nigeria's finance ministry". www.premiumtimesng.com. Retrieved 2023-09-09.
- ↑ "NBET". nbet.com.ng. Retrieved 2024-01-22.
- ↑ "Zainab Shamsuna Ahmed". EITI (in Turanci). Retrieved 2024-01-22.
- ↑ "Zainab Ahmed". World Bank Live (in Turanci). 2019-10-01. Retrieved 2021-04-24.
- ↑ AfricaNews (21 August 2019). "Nigeria's new cabinet inaugurated, president remains Petroleum minister". Africanews. Retrieved 2 September 2019.
- ↑ "Zainab Ahmed". live.worldbank.org (in Turanci). 2022-01-13. Retrieved 2023-09-20.
- ↑ TVCN (2018-09-24). "Zainab Ahmed fit for office of finance minister – GOGAN - Trending News" (in Turanci). Retrieved 2023-09-09.
- ↑ "Fashola gets Works as Ngige, Amaechi, Lai retain portfolios". The Nation Newspaper. 22 August 2019. Retrieved 24 August 2019.
- ↑ "100Women | Avance Media | Zainab Shamsuna Ahmed" (in Turanci). Retrieved 2024-01-22.
- ↑ 2019 Annual Report African Development Bank (AfDB).