Adawari Pepple

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Adawari Pepple
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

Mayu 1999 - Mayu 2003
District: Rivers South East
Rayuwa
Haihuwa Jihar rivers
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Federal Government College Ikot Ekpene (en) Fassara
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Rivers State People's Democratic Party (en) Fassara

Adawari Michael Pepple an zaɓe shi a matsayin Sanata mai wakiltan Mazaɓar Rivers ta kudu maso gabas na jihar Ribas a Najeriya a farkon jamhuriya ta huɗu ta Najeriya, inda ya tsaya takara a ƙarƙashin jam'iyyar PDP. Ya fara aiki a ranar 29 ga watan Mayun shekarar 1999.[1]

Rayuwar farko[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan ya hau kujerarsa a Majalisar Dattawa a cikin watan Yunin shekarata 1999, an naɗa Pepple a kwamitocin Man Fetur, Masana'antu (Mataimakin Shugaban), Albarkatun Ruwa, Ilimi, Ci gaban Al'umma & Wasanni da Babban Birnin Tarayya.[2] An naɗa shi Babban Mai Shari’a na Majalisar Dattawa a shekara ta 2002.[3] Pepple ya kasance mai goyon bayan canjin tsarin mulki wanda shugaban ƙasa da gwamnonin jihohi za su iya yin aiki na tsawon shekaru biyar kawai.[4] Bayan Kotun Duniya ta yanke hukuncin cewa yankin Bakassi da ake taƙaddama a kansa na ƙasar Kamaru ne, ya lura da cewa "Ƙimar rayukan ƴan Najeriya a yankin Bakassi da ma fiye da haka ya kai darajar man fetur da iskar gas a yankin".[5] A cikin bitar ayyukan sanata a cikin watan Oktoban shekarar 2002, Vanguard ta lura cewa Pepple ya gabatar da ƙudirori bakwai a Majalisar da ke yanzu.[6]

Membobin ƙungiya. kyaututtuka[gyara sashe | gyara masomin]

Michael Pepple ba mamba ne na ƙungiyar masana'antun Najeriya (MAN) kaɗai ba, shi ne shugaban ƙungiyar MAN Rivers/ reshen jihar Bayelsa.[7][8] Ya kasance wanda ya karɓi kyautar Distinguished Service Star award na Jihar Ribas (DSSRS).[9]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]