Ahmed Nuhu Bamalli

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ahmed Nuhu Bamalli
Rayuwa
Haihuwa Zariya, 8 ga Yuni, 1966 (57 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Hausawa
Harshen uwa Hausa
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a Mai wanzar da zaman lafiya
Mai martaba Sarkin Zazzau Ahmed Nuhu Bammali tare da Gwamnan Kaduna Nasir Ahmed El-rufai

Ahmed Nuhu Bamalli (an haife shi 8 ga watan Yuni, shekara ta alif ɗari tara da sittin da shida 1966) miladiya.

jami'in diflomasiyya ne na Najeriya, Banki, basaraken gargajiya kuma lauya sannan tsohon jakadan najeriya a kasar Thailand wanda shi ne Sarkin Zazzau na 19, masarautar gargajiya a Najeriya da ke da hedikwata a Zariya, Jihar Kaduna, Najeriya. Shi ne Sarki na farko daga gidan Mallawa da ke mulki tun bayan barin mulki a hannun gidan tsawon ƙarni daya baya, biyo bayan rasuwar sarkin lokacin a shekarar 1920 (shekara 100 baya) ga kakansa, Sarki Alu Dan Sidi.

Farkon Rayuwa Da Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Ahmed a garin Kwarbai Zaria, jihar Kaduna, Najeriya. Shine ɗan fari ga Nuhu Bamalli . Ahmed ya yi karatu a Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zariya inda ya samu lambar (LLB) a shekara ta 1989, sannan ya yi Digiri na biyu a kan Harkokin Ƙasa da Ƙasa da diflomasiyya daga jami'ar a shekara ta 2002. Ya sami difloma a fannin gudanarwa daga jami'ar kimiyya da fasaha ta jihar Enugu a shekarar 1998.

Ahmed yayi karatu a ɓangare da yawa na duniya; misali kan warware rikice-rikice a Jami'ar York (Birtaniya) a cikin shekarar 2009, Yayi Diploma a fannin jagoranci daga Jami'ar Oxford (UK) a shekara ta 2015. Ya kuma sami GMP daga jami'ar Harvard Business School, a shekara ta 2011.

Rayuwa Da Kwarewa[gyara sashe | gyara masomin]

Ahmed shi ne sarki na farko daga gidan mulkin Mallawa a cikin shekaru 100, bayan rasuwar Alh Shehu Idris.

Ya yi aiki a harkar banki kuma a matsayin Babban Darakta sannan daga baya ya rike mukamin Manajan Darakta na Kamfanin Kula da Tsaro da ɗab'i da ma'adanai na Najeriya.

Ya kasance kwamishina na dindindin a Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kaduna a shekarar 2015. Har zuwa lokacin da aka nada shi a matsayin sabon sarkin Zazzau, Ahmed ya rike sarautar Magajin Garin Zazzau kuma ya yi aiki a matsayin Jakadan Najeriya a Thailand, tare da amincewa da Myanmar a lokaci guda.

Ya zama sabon sarkin Zazzau a ranar 7 ga watan Oktoba,shekara ta 2020. Shine ɗan fari na Nuhu Bamalli (Magajin Garin Zazzau).

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]