Musulunci

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
(an turo daga Islama)

Addinin Musulunci Shine Addinin gaskiya shine wanda ba a bautawa kowa sai Allah Kuma Annabi Muhammad (saw) manzon sa ne Kuma Shi dan sako ne na Allah (SWT).

Annabi Muhammad (saw), tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi,[1] shi ne manzo wanda Allah ya aiko shi zuwa ga mutane baki ɗaya kuma na karshen/cikamakin annabawa a duniya domin ya sake jaddada addinin Allah, a yi imani da Allah wanda ya halicci kowa da komai. Addinin musulunci na da mabiya a duk fadin duniya kuma mafiya yawa su na zaune ne a yankin gabas ta tsakiya da yankin Afrika ta Arewa wadanda mafi yawansu Larabawa ne masu bin addinin musulunci, sai dai akwai dunbin mabiya addinin musulunci a ko'ina a fadin duniya.[2] Ma'anar Addinin Musulunci shi ne yarda da mika wuya ga Kaɗaita Allah Maɗaukakin Sarki, wato shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma annabi Muhammad Manzonsa ne (Ma'aikinsa ne), bayan haka ka/ki yarda da dukkan abubuwan da ya umarci al'umarsa haka kuma da wadanda ya hana su, da mika wuya ga umarnin Allah Ubangijin talikai, tare da tsarkaka daga kafirci (sanya kishiya wa Allah) da kafirai"Allah Madaukakin Sarki shi ya aiko Manzonsa Annabi Muhammadu (tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi) da Al Kur'ani Mai Girma domin ya zamo shiriya da rahama ga halittu baki daya, an kuma bayyana musulunci a matsayin addinin dake da saurin karin yawa a duniya a kullum wanda ke da Adadin musulmai na Duniya sun kai kusan kashi 24.1% na dukkan mutanen Duniya, wato fiye da Musulmai Biliyan Daya da Miliyan dubu dari takwas (1,800,000,000) a fadin duniya.[3]

Tarihin Addinin Musulunci[gyara sashe | gyara masomin]

Garin Makka inda aka haifi annabi Muhammad (S.A.W)

Asalin addini a duniya shi ne musulunci. Mutum na farko da Allah ya halitta,[4] Annabi Adam (alaihis salam), ya rayu ne bisa tafarkin musulunci. Dukkanin manzanni tun daga Annabi Nuhu (alaihis salam), zuwa Annabi Ibrahim, da Annabi Musa, da Annabi Isa, (alaihimus salam), musulmai ne masu kadaita Allah.[5] Sai dai gaba dayansu Allah ya aiko su ne zuwa ga al'ummominsu kadai. Annabi na karshe kuma cikamakin annabawa shi ne Annabi Muhammadu (yabo da amincin Allah su tabbata a gareshi). Allah ya aiko Annabi Muhammadu (SAW) da sako zuwa ga daukacin al'ummar duniya mutane da aljannu baki daya. An haifeshi a birnin Makkah da a yanzu ke kasar Saudi Arebiya. Annabi Muhammadu (SAW), bakureshe ne, dan Abdullahi da Amina daga tsatson Annabi Isma'ila (AS) dan Annabi Ibrahim (AS).[6]

Rukunnan Musulunci[gyara sashe | gyara masomin]

Hakika addinin musulunci an gina shi a bisa wadansu rukunai (Shika-shikai) guda biyar (5) ne kamar haka:

Kalmar Shahada[gyara sashe | gyara masomin]

Ma'anarta shi ne, shaidawa babu abin bauta bisa chanchanta da gaskiya sai ALLAH madaukakin sarki (SWT), sa'annan, Annabi Muhammad (SAW) tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi Manzon Allah ne kuma bawansa ne.[8]

Sallah[gyara sashe | gyara masomin]

Hakika Sallah ita ce ibada mafi girma a cikin addinin musulunci bayan kalmar shahada. Ita ce ibadar da mutum yake tsayawa a gaban ubangijinsa domin bautamashi, cikakken musulmi dole ne ya kasance mai yin Salloli guda biyar a Kowa ce rana, sune kamar haka:[9]

  1. Sallar Asubahi
  2. Sallar Azahar
  3. Sallar La'asar
  4. Sallar Magriba
  5. Sallar Isha'i

shi ne kashin na farko na farillah, sai kashi na biyu salloli na Sunnah, bayan rana ta fito sai raka'a biyu bayan sallar magriba sai witiri bayan shafa'i sai sallar idi qarama da sallar idi babbah su ne salloli na sunnah, sai kashi na uku sallolin nafiloli su ne suka shiga har asham ko tarawihi qiyaman-laili da dai sauransu, sune rukuni na (3) Sallah tana daya daga cikin shika-shikan Musulunci mafiya girman daraja matuka bayan Tauhidi, ana bukatar kowanne musulmi ya yi Sallah sau biyar a rana, yana mai fuskantar Ka'aba da ke kasar Saudiya.[10] A kasashen Musulmai, za'a ke jin Kiran Sallah daga Masallaci mafi kusa a yayin da lokacin Sallah ya yi. Sallah ana yinta ne cikin Natsuwa, domin a samu kyakkyawan lada.samun natsuwa na daga cikin sashe guda 6 da suke kawo cikar sallah (1)tsarki shi ne tsarkake ko wanke tufafinka da wanke jikinka da ruwa mai tsarki da kuma wanka zuchiyarka, da imani (2)daura al wallah, niyyarta da addu'o'inta, farillinta, da sunnouninta, da mustahabanta, sashe na (3)tsayuwa aguri mai kyau ko masallaci da tada iqama da kuma kudirta niyya (4)takbiri Allahu Akbar sannan kawo bissimillah da karatun fatihatil kitabi ita ce Alhamdu lillahi rabbil alamin zuwa qarshe da wata sura ko ayar da ta sauwaqa a gareka (5)ruku'u da sharuddansa tasowa daga ruku'u zuwa sujjada da sharuddanta tasowa daga sujjada zuwa zaman farko da sharruddansu sai na (6)kowane zama akwai sharadinsa har qarshe attahiyyatu lillahhi azzakiyatu lillahi zuwa qarshe))wannan ita ce sallar farillah abin da ya banbanta ta da nafila sune ababe 2 abu na farko shi ne (iqama) babu a nafila abu na biyu nafila raka a biyu(2).ninh ai

Musulmai suna Sallah a wani Masallacias

Masallaci wani wuri ne da ake bautar Allah kuma ba wata al umar musulunci da zatai rayuwa batare da masallaci ba kuma shi masallaci dakin Allah ne.

Azumi[gyara sashe | gyara masomin]

Yadda Musulmai ke buda baki bayan kai azumi

azumi wani abu ne da musulmi ke yi daga fitowar Alfijir zuwa faɗuwar rana, ta hanyar kiyaye Cin Abinci da kuma shan Ruwa da Jima'i. Da suke yi a cikin watan ramadana shi ne azumin farillah guda 29 ko 30 cikin watan9 wato watan Ramadan kuma farilla ne ga kowanne musulmi baligi, mai hankali sannan kuma mai lafiya sannan mazauni ba matafiyi ba. kuma akwai azumin sunnah kamar azumin ranar alhamis da litinin ko kuma ka yi yau gobe ka huta wato azumin Annabi Dawud har shekara ta kewayo ko kuma azumin Tasu'ah da Ashurah a wannan shi ne ne azumin farillah da sunnah) Azumi: Wani rukuni ne wanda ake nufin barin ci, da sha, da yin jima'i daga fitowan alfijir har zuwa faduwan rana. Dukkan musulmi tilas ne da ya/ta azimci watan Ramadana (watau wata na tara a lissafin kalandar musulunci).

Zakka[gyara sashe | gyara masomin]

Masara a cikin buhu wasu kayan da ake fiddama zakka

ita kuma zakkak wajibi ce ga wanda ya mallaki dukiyar da ake fitar mata da Zakka ta hanyar halal sannan ita kuma dukiyar ta kai adadi na wani lokaci da shari'a ta kayyade daga nan sai a bayar da ita ga wadansu kebantattun mutane da shari'a ta yarda da a basu. Daga cikin wadannan dukkan wanda yafidda wani abu yabayar dasunan zakkah inba halak a ciki ka jefar a tsinta ya fi lada sama da ka bada zakkah da abinda ba halak a ciki) Shi ne cire wani kayyadadden kaso, daga cikin wasu kayyadaddun dukiyoyi, a cikin wani kayyadadden lokaci ga wasu kayyadaddun mutane, domin Allah Tabaraka wa Ta'ala(SWT).

Masallacim Kudus shine guri na uku mafi tsarki a wajen musulmai a duniya

maganannan guda (1) a game dagurwarwe 3 aduniyya ALLAH yahalittah dakin ka aba atsakiyyar duniyya da tsakiyyar qassai bakwai datsakiyyar sammai7 tunkafin ahalicchi kou ina maganar baitul maqaddissi gurine kamar kache gida inda annabawan allah masuyawa suka baiyyana sai dutsin durisiyniyna inda annabi musa da haruna suka baiyana sannan yadda da Allah da annabawan Allah da littattafen Allah da alqifloulin Allah sune guda 3 adukkan inda tunaninka yakai da indabaikaiba na farko (1) dakin ka aba amakkah na 2 annabi muhammadu rasulullahi na 3 alqura anil kariymu wadannan sune 1,1,1,harqarshen duniyya dukkanwani abinda zaibiyobaya zaijiggina da dakin ka aba da alqura ani da mahammadu ma aikin Allah).

Hajji[gyara sashe | gyara masomin]

An Umarci musulmai da suje aikin hajji da ummara ita kalmar hajji alarabci kalmace tabaqo zuwa dakin Allah ko masallacin ma aikin Allah muhammadu wanda yazo daga wata qasa ko wani gari wanda ba makkah bane inzai shigo makkah akwai gurare guda 5 inda zai dauko niyyarsa dukta indaya bulloma makkah zaisamu wadannan gurare na dauko niyyar aikin hajji ko aikin ummara niyyar itache yin wanka daruwa yin alwallah yin sallah raka a 2,2,2 inkana dahali inbaka dahali raka'a 2 saikai niyyar ummarakayi ko ta hajji sannan kanemi abin hawa kashigou makkah zuwa ka aba inniyyar ummara kazo da ita saikai sallah raka'a 2 saikai dawafi kewaya 7 indahali sallah raka'a 2 sai safa da marwa suma 7 safa 4 marwa 3 kashiga marwa kagama safa sannan sai sallah raka' a 2 saikayi aski kafidda ihiramin jikinka kashiga irinkaya dakasabasawa kasauke ummara kenan akwai niyar hajji da ummara kuma ahade to yanzu kazo mitai kwanakun 6 gawatan 12 7 gawatan 12 niyyarka ko niyyarki ummara da hajji kashigo makkah ayyamin hajji da ummara kazo ka aba kayi raka atini kayi dawafi kayi safa damarwa kayi raka atiyni bazakai askiba bazaka fadda ihhiramba saka wuche aikinhajji da ihiramin dakai ummara ajikinka amman inka shigo kafin watan 12 zakayi ummara kacire ihhirami kasa kayan gida harzuwa ayyamin hajji. Shine zuwa ziyartan dakin Allah Mai Alfarma a makkah ga wanda keda iko da nufin Ibada.ko masallacin ma'aikin Allah muhammadu.

Imani[gyara sashe | gyara masomin]

shine mutun ya yarda da cewa babu wani abun bauta koma bayan (ALLAH) wanda ba a shirka dashi Ma'ana ba a hada shi da wani la'(ilaha illallahu wa hadahu lasharika lahu sashen ibada sashen sunayensa sashen siffofinsa, sashen kalamansa sashen hukuncinsa sashen kamalarsa sashen isarsa sashen matsayinsa da inda yake dukkansu basakama dana halittansa na duniya da abinda ke cikinta mutum da abinda mutum keso da wanda baya so da abinda mutum yasani da wanda bai sani ba damu da ababen da Allah ne ya haliccemu da aljannu da mala'ikunsa naso ko naqi wanda suka sani da wanda basu saniba akarbesu dukkansu haliittar Allah ne sai dabbobi nagida dana jeji na tudu dana ruwa itatuwa ko ciyayi duwarwatsu ko kuma arzikin qarqashin qasa ko nawajenta ma anar duniya da abin dake cikinta halittan Allah ne mai imani da Allah to Allah muke bautawa) karkaji ance Allah yana dakai kai masasuffar kai irin na abinda ya halitta a a karkaji ance Allah yana magana kasuffanta masa baki irin na abin daya halitta a a kokuma kasuffanta masa jiki irin na abinda ya halitta a a qaddara yanada hannu ba irin na abin daya halittaba a a ko yanada kujera ko abin zaman kujeran ba irin na halittunsa bane harzuwa al arshinsa allahhu wahidin ahadun (1)imani da mala'iku, Allah ne ya haliccesu ibadar Allah sukeyi hukuncin Allah sukebi ma ana sallah azzumi karatun qur'ani yin imani da halittun Allah imani da annabawan Allah imani da littattafan Allah sannan basa karya alqawarin da Allah ya dorasu akai su mala'iku tsakaninsu da mahaliccimmu Allah karmukusanci yimusu kamannu su dukkansu mazane ko dukkansu Mata ne ko dukkansa maza da matane Allah ne yabarwa kansa sani illah kawai su bayin Allah ne kuma ma'aikan Allah bayan bautan Allah da sukeyi su Allah yake aika tundaga sama ta 7 har ta daya 1 har cikin duniya har qasa ta 1 zuwa ta bakwai 7 mala'iku su Allah yake aike zuwa ko wace halitta wadda mukasani da wadda bamu santaba) sai yin imani da littattafan Allah littafin da Allah yaba mala'ika zuwa annabi ibrahima kalilillahi baban annabi isma'ila shi isma'ila daga gareshine harshen larabci yasamo asali sai littafin da Allah ya aiko mala'ika zuwa annabi dauda baban annabi sulemana da zabura sai littafin da Allah ya aiko mala'ika zuwa annabi musa da haruna attaura sai littafin da Allah ya aiko mala'ika zuwa annabi isa masihu dan nana maryama da injila sai littafin da Allah ya aiko mala'ika zuwa muhammadu dan abdullahi da alqur'ani qarshen aiken littattafan Allah zuwa duniya amman akwai wasu littattafan masu yawa wadanda Allah ne masani game dasu dawadanda aka aiko) sai annabawan Allah ko ma aikan Allah mutane daga annabi adamu mutum nafarko a duniya zuwa muhammadu rasulullahi an masu sunan annabi ko rasulu wasu malaman suce sunkai su dubu 8 wasu sunce sunkai dubu 6 Allah ne mafi sani game dasu abinda zamukama murike shine amba annabi wane hukunci daga Allah lokaci kaza yayi wafati loukaci kaza yabar hukuncin Allah a hannun mutanensa amatsayin amana masu mulki da masu kudi da daidaikun mutane basa buqatar wannan annabin da abinda yazo dashi sai anemi kashe wannan ilmin gabadaya kafin wadansu shekaru qa idajju sai Allah yasake aiko mala'ika dawani saban aiken zuwa wani mutum daga cikin mutane domin tunatar da sakon Allah tahakane wannan yazo ya wuce wannan yazo yawuce har annabawa dubu 8 daga annabi adamu zuwa muhammadu) sai yin imani da ranar qiyama itace ranar sakamako musulmi munyi imani da Allah muce la ilaha illallahu wahadahu lasharikalahu bamu da zabi sai abinda Allah yazaba mana sannan muce mahammadu rasulullah munyadda muhammadu ma aikin Allah ne munyadda dakin ka aba alqiblar Allah ce yadda dawadannan ababe 3 murayu acikinsu rayuwarmu taqare acikin su shine jindadin fuskantar ranar qiyama) sai alqadar ma ana kaso dadi yasame ka ko kaqi dadi yasa meka ko kuma kaqi wuya tasameka ko kaso wuya tasa meka mu qaddara daga Allah ne)kullu shai in min indillahi \faqat) Ma'anan Imani shine : abun da zuciya ta kudurta, harce yayi furuci da shi, sa'annan gabban jiki suka yi aiki da shi. Imani yana da shika-shikai guda shida (6) kamar haka : Imani da Allah, da Mala'ikunsa, da littafansa, da Manzanninsa, da Ranar karshe, da Imani da kaddara mai dadi ko marar dadi. maganar datarufe wadannan manufar addinin islama shi yakan zauna kashi 2 ajikin mutane dawanda ya zamo daga shi zuwa mahaifansa da kakanninsa kakannin kakanninsa a musulunci sukatashi dawanda mahaifansane ko kakanninsa suka shiga suka shigardashi da wanda yashiga dakansa yana qarami ko yana babba Allah yana amfanine damai kyakkyawan aiki da zuciya mai kyau tayaya zamu fahimceta dahaka karmu yadda mu maida addinin Musulunci kamar tufafi kayan sawa muyi koqari mujajirce mumai dashi jinin jikinmu inmukadaukeshi tufafi musani wuya ko dadi na iyashiga tsakaninmu da addininmu yarabamu dashi inkuwa muka maidashi jinin jikinmu bamai iya rabamu shi abadan.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://dictionary.cambridge.org/pronunciation/english/islam
  2. https://www.britannica.com/topic/Islam
  3. https://www.dictionary.com/browse/islam
  4. Lewis, Barnard; Churchill, Buntzie Ellis (2009). Islam: The Religion and The People
  5. "Muslim." Lexico. UK: Oxford University Press. 2020
  6. Esposito (2000), pp. 76–77
  7. Gibb, Sir Hamilton (1969). Mohammedanism: an historical survey. Oxford University Press. p. 1. ISBN 9780195002454
  8. https://books.google.com/books?id=dbSPOoQfu0IC&pg=PA68
  9. "Tawhid". Encyclopædia Britannica. Archived from the original on 7 November 2021. Retrieved 17 September 2021
  10. Gimaret, D. "Tawḥīd". In Encyclopaedia of Islam (2nd ed.) (2012). doi:10.1163/1573-3912_islam_SIM_7454