John Kpera

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
John Kpera
Gwamnan jahar benue

ga Janairu, 1984 - ga Augusta, 1985
Aper Aku (en) Fassara - Jonah David Jang
Gwamnan jahar Anambra

ga Maris, 1976 - ga Yuli, 1978 - Datti Abubakar
Rayuwa
Cikakken suna John Kpera
Haihuwa 3 ga Janairu, 1941 (83 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Tiv
Harshen uwa Harshen Tiv
Karatu
Harsuna Turanci
Harshen Tiv
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Digiri Janar

Birgediya-Janar John Atom Kpera (An haife shi a ranar 3 ga watan Janairun shekarar 1941) ya kasance Gwamna Soja na farko a Jihar Anambra a Nijeriya daga Maris 1976 zuwa Yulin 1978, bayan an kirkireshi daga tsohuwar Jihar Gabas ta Tsakiya a lokacin mulkin soja na Janar Olusegun Obasanjo. Daga baya ya kasance Gwamnan Soja na Jihar Benuwai daga Janairun shekarata 1984 zuwa Agustan shekarar 1985 a lokacin mulkin soja na Manjo-Janar Muhammadu Buhari.[1]

Farkon Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi John Atom Kpera a ranar 3 ga watan Janairun shekarar 1941 a Mbatierev, karamar hukumar Gboko a cikin jihar Benuwai ta yanzu. Ya halarci Kwalejin Katsina-Ala, yanzu ta zama Kwalejin Gwamnati ta Katsina-Ala, (1956–1961) don karatun sakandare. Bayan ya shiga aikin soja ya halarci Makarantar Koyon Soja ta Haile Selasie, Habasha a shekarar 1962 domin horar da shi kan aikin soja, kuma an ba shi mukamin Laftana na 2 a kungiyar Injiniya a shekarara 1965. Ya rike mukamai da mukamai daban-daban da suka hada da Injiniya Brigade Commander, Kwamandan Squadron, Regimental Commander, da Kwamanda, Corps of Engineers.

Aikin Soja[gyara sashe | gyara masomin]

Ya taka rawa a juyin mulkin soja na farko a Najeriya a ranar 15 ga watan Janairun shekarar 1966, inda ya taimakawa Chukwuma Kaduna Nzeogwu a yunƙurin kifar da gwamnatin yankin Arewa. Juyin mulkin bai yi nasara ba a manufofinta, amma ya haifar da Manjo-Janar Johnson Aguiyi-Ironsi wanda ya hau mulki a gwamnatin soja ta farko ta Najeriya.

An naɗa shi Gwamnan Soja na Jihar Anambra daga watan Maris shekarar 1976 zuwa watan July shekara ta 1978, a lokacin mulkin soja na Olusegun Obasanjo. Daga nan kuma ya zama Kwamandan Makarantar Sojoji ta Hedikwatar injiniyoyi, sannan Daraktan Manpower, Hedikwatar Sojojin Nijeriya ya biyo baya.

A ranar 4 ga watan Janairun shekarar 1984 aka nada shi Gwamnan Soja na Jihar Benuwai, shugaban soja na farko da aka haifa a jihar da ya mulki jihar. Ya kirkiro wata manufa ta tilastawa mutane tsabtace muhallinsu karkashin kulawar sojoji, aikin da magadansa suka kiyaye. A lokacin da aka sauke shi daga mukaminsa na gwamna, ya ce game da baitul malin jihar ya bar shi fanko domin ya sadu da shi fanko.[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. http://www.worldstatesmen.org/Nigeria_federal_states.htm
  2. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2016-03-03. Retrieved 2021-07-25.