Moustapha Kama
Moustapha Kama | |
---|---|
Ɗan Adam | |
Bayanai | |
Jinsi | namiji |
Ƙasar asali | Senegal |
Suna | Moustapha (en) |
Sunan dangi | Kama |
Shekarun haihuwa | 28 ga Janairu, 1992 |
Harsuna | Faransanci |
Sana'a | taekwondo athlete (en) |
Wasa | Taekwondo |
Moustapha Kama (an haife shi ranar 28 ga watan Janairun 1992) ƙwararren ɗan wasan taekwondo ne kuma ɗan Senegal ne. Shi ne wanda ya lashe lambar yabo sau biyu a gasar wasannin Afirka kuma ya samu lambar tagulla a wasannin haɗin kai na Musulunci. Ya kuma lashe lambobin yabo a gasar Taekwondo ta Afirka.
A cikin shekarar 2018, a gasar Taekwondo ta Afirka ta shekarar 2018 da aka gudanar a Agadir na ƙasar Morocco, ya lashe lambar azurfa a gasar tseren kilo 54 na maza.[1]
A cikin shekarar 2019, ya wakilci Senegal a gasar cin kofin Afrika na shekarar 2019 da aka gudanar a Rabat, Morocco, kuma ya lashe lambar tagulla a gasar maza ta kilogiram 54.[2] A cikin shekarar 2020, ya yi takara a gasar tseren kilo 58 na maza a gasar Taekwondo ta Afirka ta shekarar 2020 na cancantar shiga gasar Olympics a Rabat, Morocco ba tare da samun cancantar shiga gasar Olympics ta bazara ta shekarar 2020 a Tokyo, Japan.[3]