Ahmad Bamba

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ahmad Bamba
Rayuwa
Haihuwa 1940
ƙasa Najeriya
Mutuwa jihar Kano, 7 ga Janairu, 2022
Sana'a
Sana'a Malami

Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba ( c. 1942 – 7 January 2022) Larabci: أحمد بن محمدAhmad ibn Muḥammad malamin addinin musulunci ne dan kasar Ghana. Ya yi aiki a matsayin malami a Jami'ar Bayero, Kano. Ya karantar da Hadisi Sahihul Bukhari a Masallacinsa (Darul Hadis (Gidan Hadisi) da ke Tudun Yola Jihar Kano Najeriya. Ana kuma kiransa da Qala Haddasana,[1] kalmar da ya yawaita ambata a lokacin koyarwarsa.[2][3][4]

Rayuwar farko[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Sheikh Dr. Ahmad Bamba a shekara ta alif dubu daya da dari Tara da arba'in (1940). Ya girma a Alabar AEB ko Nguwan Gonjawa, wani yanki a cikin birnin Kumasi na Ghana. Mahaifinsa shi ne Muhammad Ibrahim Bamba, mahaifiyarsa kuwa su ne Hajia Khadijah (Mama Adizatu) da Hajiya Fatima (Mama Hajia) 'ya'yan Mma Gyamata, diyar malami ce kuma sarkin Gonja na farko a Kumasi, Malam Sani.

Farkon karatunsa na Islamiyya ya zo a Wataniyya karkashin jagorancin Sufi, Alhaji Baba Al-Waiz (Babal-Waiz) a Kantudu. Ya kammala karatunsa a karkashin koyarwar gidan mahaifinsa. Ya kuma ci gaba da karatunsa na fiqhu (Fiqhu) sannan ya fara da Al-Ishmawiy karkashin jagorancin Malam Amadu Langonto (ɗan Baba Ibrahim/Ibrah kuma Imamin Gonja). Daga baya ya yi karatu a wajen mai rayar Sunna na farko a Kumasi, Sheikh Abdul Samad Habibullah. Abokan karatunsa sun haɗa da Malam Imrana Musah, marigayi babban Limamin yankin Ashanti, Ķhåĺifs na Wataniyya na yanzu da marigayi Malam Muntari, babban limamin unguwar Dagomba, Alhaji Lawal na Baba Abbas (wanda aka fi sani da Alhaji Nuhu Abbas), Malam Zakari. Alhaji Nuhu Kotokoli, Ustaz Umar, Limamin Al'ummar Yadiga, Alhaji Siidi, Malam Muhammad Danraz, da Malam Ɗan Azumi.

Abokin aikinsa Malam Muntari ya shawarce shi da ya yi karatu tare da Sheikh Abdul-Samad, bayan ya koka da tazarar Alabar zuwa Garin Accra (Oforikrom) inda malaminsa Malam Amadu yake zaune. Muntari ya kasance yana karatu a makarantar Sheikh Abdul Samad.

A cewar Muntari, Bamba tare da koyon sana’ar dinkin da zane daga Malam Awudu, shugaban al’ummar Grunshi da Sissala a Kumasi. Bugu da kari, ya kuma yi sana’ar shanu wadda ya koya daga Muntari wanda sana’ar mahaifinsa sana’ar shanu ce.

Duk da shagaltuwarsa a cikin kasuwanci, ya ɗauki karatunsa da muhimmanci. Bayan koyo daga Sheikh Abdul Samad, malaman Masar sun samu tallafin gwamnatinsu sun zo Kumasi suka kafa makarantar Markaz Al-Sharif. Bamba da abokin aikinsa Muntari sun yi rajista. Malamansa sun lura cewa Bamba yana da ƙarfin da ba a saba ba. An ba shi damar yin karatu a Masar. Ya yi zaman wata daya kacal bayan ya yanke shawarar yin karatun Hadisi a Jami'ar Musulunci ta Madina inda ya samu digirin digirgir na BA, MA da PhD.

Bamba yana cikin daliban Sheikh Hamad Bin Muhammad Al Ansaari. Jami’ar Bayaro ta Kano ta ba Bamba shawarar a matsayin babban Muhadith, inda ya yi maraba da shi kuma ya zauna a matsayin malami kuma malami har zuwa rasuwarsa.[5][6]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Ya kasance malami a jami'ar Bayaro a tsangayar karatun addinin musulunci inda kuma ya karantar da Hadisi. Wannan ya kai ga samar da masallacin Darul Hadith' (Gidan Hadisi) inda ya ci gaba da karantarwarsa bayan ya yi ritaya.

Rasuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Ya rasu a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano da ke Jihar Kano a ranar 7 ga watan Janairu,shekara ta 2022. Ya rasu yana da shekaru 79.[7][8]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]