Dahiru Mohammed
Dahiru Mohammed | |||
---|---|---|---|
ga Janairu, 1992 - Nuwamba, 1993 ← Abu Ali (Janar soji) - James Kalau → | |||
Rayuwa | |||
Haihuwa | Yamaltu/Deba, 24 Satumba 1942 (81 shekaru) | ||
ƙasa | Najeriya | ||
Ƙabila | Hausa | ||
Harshen uwa | Hausa | ||
Karatu | |||
Makaranta |
Vanderbilt University (en) Jami'ar Ahmadu Bello | ||
Harsuna |
Turanci Hausa Pidgin na Najeriya | ||
Sana'a | |||
Sana'a | ɗan siyasa | ||
Employers | Africa Bank Capitalisation Fund project (en) | ||
Mamba |
Nigerian Institute of Management (en) American Economic Association (en) Southern Economic Association (en) Chartered Institute of Bankers of Nigeria (en) | ||
Imani | |||
Jam'iyar siyasa | Peoples Democratic Party |
Dahiru Mohammed (an haife shi a ranar 24 ga watan Satumba a shekara ta alif ɗari tara da arbain da biyu 1942Ac) ɗan siyasa ne. Gwamnan jihar Bauchi ne daga watan Janairu a shekara ta 1992 zuwa watan Nuwamba a shekara ta 1993. Alhaji Dahiru Mohammed Deba (an haife shi a shekara ta 1942) ɗan siyasan kasar Nijeriya ne wanda aka zaɓa Gwamnan Jihar Bauchi, Nijeriya tsakanin watan Janairun shekara ta 1992 zuwa Nuwamba shekara ta 1993 a lokacin Jamhuriya ta Uku ta Nijeriya, inda ya bar ofis bayan juyin mulkin soja da ya kawo Janar Sani Abacha kan mulki.[1]
Farkon rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]
An haifi Deba a ranar 24 ga watan Satumba shekarara ta alif 1942, a Deba, sannan a jihar Bauchi yanzu kuma a jihar Gombe. An ba shi sarautar gargajiya ta Wazirin Deba.[2]
Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]
An zabi Dahiru gwamna a shekara ta alif 1991 a karkashin kungiyar National Republican Convention (NRC).[3] Nasarorin da ya samu a matsayin gwamna sun hada da gina asibitoci, da suka hada da babban asibitin Alkaleri da cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko a Dambam, Zambuk, Bambam da Burra, da kuma gidauniyar asibitin turawa na Gombe. Gwamnatinsa ta gina sabbin otal-otal guda biyu a Jama'are da Ningi. Ya ƙaddamar da Asusun Amincewar Ilimi na Naira miliyan 200. Wa'adin mulkinsa ya yanke a watan Nuwamba na shekara ta alif 1993 lokacin da Janar Sani Abacha ya kwace mulki.[4]
Dahiru ya zama memba na Democratic Party of Nigeria (DPN), wanda aka kafa a zamanin mulkin Abacha. Ya taimaka wa Danjuma Goje, wanda daga baya ya zama gwamnan jihar Gombe, a zaben Sanatan shekarar 1998 da Abacha ya yi, wanda aka soke bayan mutuwar Abacha.[5]
Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]
- ↑ http://www.worldstatesmen.org/Nigeria_federal_states.htm
- ↑ http://allafrica.com/stories/201003030213.html
- ↑ http://allafrica.com/stories/200911110210.html
- ↑ https://web.archive.org/web/20110725042938/http://www.bauchistategov.org/pastexecutivecouncil.html
- ↑ http://odili.net/news/source/2008/nov/15/202.html[permanent dead link]