Jump to content

Muhammad Garba

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Muhammad Garba
Rayuwa
Haihuwa Kano, 25 Nuwamba, 1964 (59 shekaru)
Sana'a
Sana'a ɗan jarida

Muhammad Garba dan jarida ne kuma Dan Najeriya,[1] kuma dan siyasa daga jihar Kano wanda shine kwamishinan yada labarai.[2] kuma memba na Kwamitin Gudanarwa a Kungiyar Yan Jarida ta Duniya.[3]

Rayuwar farko da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Muhammad a ranar 22 ga watan Nuwambar shekara ta alif dari tara da sittin da hudu (1964) a Yakasai Quarters a Kano Municipal ta jihar Kano. Ya halarci Makarantar Firamare ta Kofar Nassarawa da Kwalejin Malamai, Sumaila ya yi Digiri na daya da na biyu a Jami'ar Bayero Kano.[4][5]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Muhammad ya fara aikin jarida a shekarar 1989 tare da Kamfanin Dillancin Labarai na Triumph, Kano a matsayin dan jarida kuma ya yi aiki a jihohi daban-daban na tarayya a matsayin wakilin. Daga baya ya girma a cikin aikinsa har ya zama Babban Edita, Editan Labaran Rukuni, da Mataimakin Edita.[4] Ya kuma taba zama memba na Hukumar Edita na Jaridun Kasa da dama. Muhammed Garba ya rike mukamai daban-daban da suka hada da Sakataren Yada Labarai na Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai a shekarar 1993 da Sakataren Yada Labarai na Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje a shekarar 1999 zuwa 2003. Ya fara fafutukar sa na kungiyar ne a matsayin shugaban kungiyarsa ta Chapel-The Triumph, wacce ke karkashin kungiyar Yan jarida ta Najeriya (NUJ), jihar Kano. Daga baya aka zabe shi shugaban majalisar jiha na a wa’adi biyu kuma ya kasance mataimakin shugaban kungiyar na kasa, sannan ya zama shugaban kungiyar Yan jarida ta Najeriya NUJ a shekarar 2009. Muhammad ya kasance shugaban kungiyar Yan jarida ta yammacin Afirka (WAJA) wanda aka zaɓa a Bamako, Mali kuma shine shugaban kungiyar Yan siyasan jarida ta Afrika (FAJ) wanda aka zaba a Casablanca, Morocco 2009. Muhammad memba ne na Kwamitin Gudanarwa na Kungiyar Yan Jarida ta Duniya (IFJ) wanda aka zaba a Dublin, Ireland. Dr Abdullahi Umar Ganduje ya nada Muhammad kwamishinan yaɗa labarai a shekarar 2015.[6][7][8]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://platinumpost.ng/2020/01/10/profile-muhammad-garba-the-kano-state-government-imagemaker/
  2. https://www.dailytrust.com.ng/kano-ganduje-retains-some-former-commissioners-in-new-cabinet.html
  3. https://thetriumphnews.com/meet-kanos-new-commissioners-i/[permanent dead link]
  4. 4.0 4.1 "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2020-12-03. Retrieved 2021-05-20.
  5. https://platinumpost.ng/2020/03/02/the-journey-of-a-versatile-journalist-to-the-peak/
  6. https://www.kanostate.gov.ng/?q=portfolio/ministry-information-internal-affairs Archived 2021-05-20 at the Wayback Machine
  7. https://guardian.ng/news/kwankwaso-others-made-gandujes-commissioners-list/
  8. https://dailypost.ng/2019/11/05/ganduje-swears-in-new-commissioners/